Yusufu da Bala
Gata nan gata nanaku. Ta zo mu ji ta.
Akwai wasu yara su biyu; Yusufu da Bala, wata rana ana biki a gidansu, sai aka aike su su je daji su yanko yakuwar miya. A kan hanyarsu ta tafiya sai suka ci karo da wani Æ™aton zakara da ganga rataye a wuyansa. Sai zakaran ya tambaye su, “Yara-yara ina za ku je ne?”, sai suka ce da shi, “Za mu je mu yanko yakuwa ne”, sai ya ce, “Na yi muku É—an kiÉ—a ku ji?”, sai suka ce, “e”, sai ya fara”.
Tamagungun-tamagungun muƙut sai ya haɗiye su.
Can a gidansu yaran kuwa, aka ga yara sun jima basu dawo ba, saboda haka sai iyayensu mata suka bisu, sai suma suka haɗu da wannan zakara. Da zakara ya gansu kawai sai ya fara waƙa:
Zakara: Ku-ku-ku ina za ku, tarmanamana
Mata: Neman ‘ya’yanmu za mu tarmanamana
Zakara: Su ‘ya’yan ina za su, tarmanamana
Mata: ÆŠiban yakuwa za su, tarmanamana
Zakara: ÆŠiban yakuwar mene, tarmanamana
Mata: ÆŠiban yakuwar taushe, tarmanamana
Zakara: In yi muku ɗan kiɗa ku ji? Tamagun-tamagun, muƙut sai ya haɗiye matan suma.
Da jama’ar gari suka ga shiru, yara basu dawo ba, haka nan ma iyayensu mata, sai dukkan mutanen garin har da sarkinsu suka fita neman su. Da suka haÉ—u da wannan zakara suma duk sai ya haÉ—iye su.
Can sai ga wani mutum shi kaÉ—ai ya fito daga wani garin, yana kan hanyarsa ta tafiya, sai ya haÉ—u da wannan zakara, da suka haÉ—u, sai zakara ya yi yunÆ™urin haÉ—iye wannan mutumi, bai gama haÉ—iye shi baki É—aya ba, sai wannan mutumi ya hango waÉ—annan jama’a da wannan zakara ya haÉ—iye, ganin haka dama hannun mutumin nan akwai wuÆ™a, saboda haka sai ya Æ™ara dagewa har sai da ya farka cikin wannan zakara ya faÉ—i matacce, sauran jama’a kuma kowa ya fito ya kama gabansa.
Tunƙurunƙus, badan Gizo ba da na yi ƙarya