ASARA GA WANDA BA YA SALLOLIN NAFILA


ASARA GA WANDA BAYA YIN SALLOLIN NAFILA

*1-YIN NAFILA RAKA'A 12 A KOWANE YINI*

Banbanci tsakanin wanda yake kiyaye Sallolin nafila na yini da dari guda 12,ashe shekara daya yana da;
*"Raka'a 4320 na nafila a shekara daya"*.

Ashekara goma yana da;
*Raka'a 43,200*

Ashe kara Talatin yana da;
*Raka'a 129,600*.

Wanda bayayin nafila yayi Asarar dukkan wadan nan baki daya.

*2-KIYAYE YIN WUTRI RAKA'A DAYA A KOWANE DARE*

Banbanci tsakanin wanda yake yin wutri aqalla sau daya akowane dare da wanda bayayi.

Wanda yakeyin wutri da raka'a daya a kowane dare,Shekara guda yana da;
*Raka'a 360*

Ashe kara goma yana da;
*Raka'a 3,600*

Ashe kara Talatin yana da;
*Raka'a 10,800*

Wanda babayi duk shekara yana yin asarar raka'a 360 duk shekara.

Ashekara goma asarar raka'a 3,600.

Ashekara Talatin asarar raka'a 10,800.

*3-KIYAYE RAKA'A BIYU NA WALLAHA KOWANE YINI*

Awanda yake kiyaye akalla raka'a biyu na sallar wallaha a kowane yini,yana samun;

Ashekara daya yana da;
*Raka'a 720*

Ashekara goma yana da;
*Raka'a 7,200*

Ashe kara Talatin yana da;
*Raka'a 21,600*

Wanda baya yin Sallar wallaha ashekara daya yana asarar:
*Raka'a 720*

Ashekara goma yana asarar:
*Raka'a 7,200*

Ashekara Talatin yana asarar;
*Raka'a 21,600*

Ka mu manta akowace raka'a akwai;
*Sujada guda biyu*
Wanda sujada itace mafi lokacin da bawa yake samun kusanci zuwa ga Allah.Kuma Allah yafi amsa adduar bawansa a wannan lokaci.

*Ruku'u daya*
Wanda itace mafi girma nuna kaskancin bawa zuwa ga Allah,kuma shine lokacin mafi girma na girmama Allah.

*Karatun Fatiha*
Wadda itace babban rukune daga cikin rukunnan sallah baki daya bayan Niyya,kuma itace sura mafi girma daga cikin surorin Alqurani baki daya.

Kuma kada mu manta da;
*Yin kowace sujada guda daya tana yiwa mutum sanadiyyar shiga aljanna,kuma babu wata sujada da zakayi face Allah ya daukaka matsayinka da darajarka.

Manzon Allah ﷺ yana cewa;
*(Ina yi maku Umarni da Wasiyya akan ku yawaita yin Sujada,domin kai bazaka taba yin Sujada ga Allah ba face sai Allah ya daukaka Darajarka kuma ya kankare maka zunubanka)*
@رواه مسلم.

Kuma kada mu manta Sahabin da Manzon Allah ﷺ yace dashi;
*(Roki??)*sai yace ina rokon na zama makwabcinka a aljanna,sai Manzon Allah ﷺ yace;
*(Ka taimakeni a kanka da yawaita yin Sujada)*
Ma'ana yawaita yin nafila.
@صحيح الجامع.

Kuma kada mu manta da cewa;
*Ana cire gurbin abinda ya baci ko ya kasa na sallar farillah ana cike sane da nafila*

Manzon Allah ﷺ yana cewa;
*(Farkon abinda za'a fara yiwa bawa na aiyukansa hisabi a ranar alqiyama shine Sallah,idan taci kuma tayi kyau to ya rabauta kuma ya tsira,amma idan ta samu tawaya to ya tabe yayi Asara,sai Allah yace kuyi dubi acikin aiyukan bawana shin yana yin Sallar nafila sai ku cike gurbinsu........)*
@صححه الألباني في صحيح سنن الترمذي.

*Mafi alkhairin aiki awajan Allah shine wanda aka dauwama ana yinsa komai kankantarsa*

Allah ne mafi sani.

Allah ya bamu ikon kiyayewa ya bamu kiriya daga wannan asara.
Post a Comment (0)