KHUƊUBAR MASJIDIS SALAFIYYA BIU BORNO STATE: 19/SHA'ABAN/1442-HJRY 02/APRIL/2021-MLDY




KHUƊUBAR MASJIDIS SALAFIYYA BIU BORNO STATE:
19/SHA'ABAN/1442-HJRY
02/APRIL/2021-MLDY


GABATARWA:--- Abubakar BN Mustafa Biu 

♦️TOPICπŸ‘‰πŸΌ [[ ƘARAMIN YARO YAJA MAHAIFINSA MASALLACI]] 

➖MUQADDIMA✔️
  Yaku bayin ALLAH! mu bautawa ALLAH SW mudaina tukuna, dominfs ibada shine kariya kaΙ—ai daga azabar ALLAH, 
πŸ’‘ALLAH SW yace <<ya waΙ—anda sukayi imani kukare kawunanku da iyalanku daga wutanda makamashinta mutanene da duwatsu...... >> {SRT TAHRIM-6}

➖ƘISSAR YARONDA YAZAMA SANADIN SHIRIYAN GIDANSU✔️
  Wannan Ζ™issar SHEIKH IBRAHIM AL-FARIS ya kawo cikin littafinsa
 [Ω‚Ψ΅Ψ΅ Ω…ΨΉΨ¨Ψ±Ψ© للأطفال]
YACE wannan Ζ™issar da gaskene kuma an yaΙ—ata a kafofin yaΙ—a labarai= Ζ™aramin yarone Ι—an aji 3 a primary, Malamansa da matasan Makarantar suna kwaΙ—aitar dasu ibada da kuma salloli a jam'i (Masallaci) musammanma sallar asuba, tarbiyyannan yayi tasiri ga yaron, amma kash! Wa zai riΖ™a tayar dashi❓Babansa❓Mamarsa a'a, baswa tashiwa don sallar asuba,
  Yaron ya yanke wata shawara mai haΙ—ari, shine zai hana idonsa barci har asuba, haka yayi, yana jin Ζ™iran sallar asuba yafito yabuΙ—e Ζ™ofa, yacika da firgici da tsoro yayinda yaga duhu kuma titinsu tsit ba kowa, kwatsam yaji takun tafiya Ζ™asa Ζ™asa, dattijone ke tafiya a hankali tokare da sandarsa tafin Ζ™afarsa baya taΙ“a Ζ™asa sosai, yaron yadubeshi sai yaganeshi ashe kakan abokinsane Ahmad, yabi bayan dattijon da sanΙ—a ba tareda yasaniba har masallaci sukayi salla haka yabiyoshi da sanΙ—an har gida yashiga gida yakulle yakwanta yataΙ“a barci yatashi yatafi makaranta, haka yacigaba a kullum har tsawon zamani, ba wanda yagane a gidansu saidai suna ganin yana yawan barcin rana,
  Kwatsam! Yaro yaji labarin mutuwar yayita kuka mai tsanani na tashin hankali don rasa damar zuwa masallaci don asuba, Hankalin mahaifinsa ya tashi Ζ™warai, harma yake cewa= ya kake kukan mutuwar bare, shifa ba babanka bane ba mamarkaba ba Ι—an uwankaba, sai Ζ™aramon yaron yace= kaiconka baba da kai kamutu yafi mini sauΖ™in baΖ™in ciki akan mutuwar dattijonnan!
  Hankalin baban Ζ™aramin yaronnan ya tashi sosai don furucin yaronsa, ya matsa masa da tambayan dalili, sai yaron yace= dattijonnan ina bin bayansa ba da saninsaba ina zuwa asuba...... yakwashe labari kaf yabasu, nan take iyayensa suka fashe da kuka, babannasa hawaye yana shaΖ™eshi kamar ransa zai fita, haΖ™iΖ™a wannan lamarin yayi tasiri a rayuwarsu, yacanza rayuwarsu yazama silar shiriyarsu, daga wannan ranan baban zai tashesu sutafi masallaci suyi sallar asuba, gidan yazanto salihin gida ALHAMDULILLAH, 

➖DAGA DARUSSAR ƘISSAR

 Sakacin iyaye a addini da rashin kamun kansu yana damun 'ya'yansu

 Nagartattun Makarantu da Malamai da abokai suna tasiri matuΖ™a don gyaran tarbiyya

 ΖŠa nagari babban arziΖ™ine ga iyayensa a rayuwarsu da mutuwarsu

 lura da yanayin yara- na daga mafi girman haΖ™Ζ™in yaran akan iyayensu

 lura da shige da ficen yara musammanma cikin dare

 Yaro da Mahaifinsa kowannensu na iya shiryuwa da Ι—an uwansa

➖RUFEWA
  Bayin ALLAH, muyi tanadi domin RAMADAN ya kusanto, kwanaki 10 kacal suka rage, mu fuskanceta da treatment na cututtukanda ka iya hanamu azumi, mu fuskanceta da kyakkyawar Ζ™udurin rayata da ibadoji, in mun iso da rai sai muyi, in mun mutu kuma musami ladan niyya, 
  Kuma muna jan hankalin uwaye mata masu zuwa jinya asibiti suguji zama babu sutura ta musulunci watama ba riga a Ι—akin jiyya, susanifa asibitin ba Ι—akinsu bane, ai koda Ι—akinkine ba muharraminkiba zai shigo wajibine kirufe jikinki, ballantana asibiti wanda samada maza 100 zasu shigo dubiya, su ma maza suji tsoron ALLAH wajen shiga Ι—akin jiyyar mata a asibiti donfa ba matansune kaΙ—ai a Ι—akinba, kada su shiga saida buΖ™atar shigowan kuma su runtse idanunsu kuma suyi saurin ficewa in sun kammala, 

ALLAH YASA MU WANYE LAFIYA- iyayenmu da 'ya'yanmu
AMIN 

viaAbubakar BN Mustafa BiuπŸ‘‡πŸ‘‡

Post a Comment (0)