KHUΖUBAR MASJIDIS SALAFIYYA BIU BORNO STATE:
19/SHA'ABAN/1442-HJRY
02/APRIL/2021-MLDY
GABATARWA:--- Abubakar BN Mustafa Biu
♦️TOPICππΌ [[ ΖARAMIN YARO YAJA MAHAIFINSA MASALLACI]]
➖MUQADDIMA✔️
Yaku bayin ALLAH! mu bautawa ALLAH SW mudaina tukuna, dominfs ibada shine kariya kaΙai daga azabar ALLAH,
π‘ALLAH SW yace <<ya waΙanda sukayi imani kukare kawunanku da iyalanku daga wutanda makamashinta mutanene da duwatsu...... >> {SRT TAHRIM-6}
➖ΖISSAR YARONDA YAZAMA SANADIN SHIRIYAN GIDANSU✔️
Wannan Ζissar SHEIKH IBRAHIM AL-FARIS ya kawo cikin littafinsa
[ΩΨ΅Ψ΅ Ω
ΨΉΨ¨Ψ±Ψ© ΩΩΨ£Ψ·ΩΨ§Ω]
YACE wannan Ζissar da gaskene kuma an yaΙata a kafofin yaΙa labarai= Ζaramin yarone Ιan aji 3 a primary, Malamansa da matasan Makarantar suna kwaΙaitar dasu ibada da kuma salloli a jam'i (Masallaci) musammanma sallar asuba, tarbiyyannan yayi tasiri ga yaron, amma kash! Wa zai riΖa tayar dashi❓Babansa❓Mamarsa a'a, baswa tashiwa don sallar asuba,
Yaron ya yanke wata shawara mai haΙari, shine zai hana idonsa barci har asuba, haka yayi, yana jin Ζiran sallar asuba yafito yabuΙe Ζofa, yacika da firgici da tsoro yayinda yaga duhu kuma titinsu tsit ba kowa, kwatsam yaji takun tafiya Ζasa Ζasa, dattijone ke tafiya a hankali tokare da sandarsa tafin Ζafarsa baya taΙa Ζasa sosai, yaron yadubeshi sai yaganeshi ashe kakan abokinsane Ahmad, yabi bayan dattijon da sanΙa ba tareda yasaniba har masallaci sukayi salla haka yabiyoshi da sanΙan har gida yashiga gida yakulle yakwanta yataΙa barci yatashi yatafi makaranta, haka yacigaba a kullum har tsawon zamani, ba wanda yagane a gidansu saidai suna ganin yana yawan barcin rana,
Kwatsam! Yaro yaji labarin mutuwar yayita kuka mai tsanani na tashin hankali don rasa damar zuwa masallaci don asuba, Hankalin mahaifinsa ya tashi Ζwarai, harma yake cewa= ya kake kukan mutuwar bare, shifa ba babanka bane ba mamarkaba ba Ιan uwankaba, sai Ζaramon yaron yace= kaiconka baba da kai kamutu yafi mini sauΖin baΖin ciki akan mutuwar dattijonnan!
Hankalin baban Ζaramin yaronnan ya tashi sosai don furucin yaronsa, ya matsa masa da tambayan dalili, sai yaron yace= dattijonnan ina bin bayansa ba da saninsaba ina zuwa asuba...... yakwashe labari kaf yabasu, nan take iyayensa suka fashe da kuka, babannasa hawaye yana shaΖeshi kamar ransa zai fita, haΖiΖa wannan lamarin yayi tasiri a rayuwarsu, yacanza rayuwarsu yazama silar shiriyarsu, daga wannan ranan baban zai tashesu sutafi masallaci suyi sallar asuba, gidan yazanto salihin gida ALHAMDULILLAH,
➖DAGA DARUSSAR ΖISSAR
Sakacin iyaye a addini da rashin kamun kansu yana damun 'ya'yansu
Nagartattun Makarantu da Malamai da abokai suna tasiri matuΖa don gyaran tarbiyya
Ζa nagari babban arziΖine ga iyayensa a rayuwarsu da mutuwarsu
lura da yanayin yara- na daga mafi girman haΖΖin yaran akan iyayensu
lura da shige da ficen yara musammanma cikin dare
Yaro da Mahaifinsa kowannensu na iya shiryuwa da Ιan uwansa
➖RUFEWA
Bayin ALLAH, muyi tanadi domin RAMADAN ya kusanto, kwanaki 10 kacal suka rage, mu fuskanceta da treatment na cututtukanda ka iya hanamu azumi, mu fuskanceta da kyakkyawar Ζudurin rayata da ibadoji, in mun iso da rai sai muyi, in mun mutu kuma musami ladan niyya,
Kuma muna jan hankalin uwaye mata masu zuwa jinya asibiti suguji zama babu sutura ta musulunci watama ba riga a Ιakin jiyya, susanifa asibitin ba Ιakinsu bane, ai koda Ιakinkine ba muharraminkiba zai shigo wajibine kirufe jikinki, ballantana asibiti wanda samada maza 100 zasu shigo dubiya, su ma maza suji tsoron ALLAH wajen shiga Ιakin jiyyar mata a asibiti donfa ba matansune kaΙai a Ιakinba, kada su shiga saida buΖatar shigowan kuma su runtse idanunsu kuma suyi saurin ficewa in sun kammala,
ALLAH YASA MU WANYE LAFIYA- iyayenmu da 'ya'yanmu
AMIN
viaAbubakar BN Mustafa Biuππ
