HUKUNCIN FUSKANTAR ALKIBLA YAYIN BIYAN BUKATA A BANDAKI

HUKUNCIN FUSKANTAR ALKIBLA YAYIN BIYAN BUKATA A BANDAKI


:
*TAMBAYA*❓
:
salam ga tambaya yaya hukuncin mutumin da ya kalli alkibila yayin da yake biyan bukatarsa amma kuma yana bandaki ba'a fili yake ba ?
:
*AMSA*👇
:
To kanina, malamai sun yi sabani akan mas'alar, Abu-hanifa ya hana hakan , Malik ya tafi akan cewa mutukar a gida ne to babu laifi, saboda hadisin Abdullahi dan Umar wanda yake cewa : "Na hau dakin Hafsa sai na ga Annabi s.a.w. yana biyan bukatarsa, yana fuskantar Sham ya kuma juyawa alkibla baya", kamar yadda Bukari ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 145.
Saidai abin da ya fi shi ne : kar mutum ya fuskanci alkibla, ko da a gida ne, saboda hadisin Abu-ayyub wanda Annabi s.a.w. yake cewa : "Idan kuka zo yin bahaya to kada ku fuskanci alqibla kada kuma ku bata baya" Bukhari a hadisi mai lamba ta : 394 da muslim a hadisi lamba ta : 264
Duba bidayatul-mujtahid 1\115.

Tabbas rashin kallon alqibla yayin biyan bukata shi ne ya fi, saboda hadisin da ya gabata da kuma fita daga sabanin malamai, don haka idan mutum zai gina shadda a gidansa zai yi kyau ya kautar da ita daga alkibla .

Allah ne mafi sani .

Dr Jamilu Zarewa 

Ku kasance damu cikin wannan group domin ilimintarwa, Fadakarwa da Tunatarwa a Sunnah.
TELEGRAM:👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
FACEBOOK👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
WHATSAPP👇 
https://wa.me/+2348087788208

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚَ
Post a Comment (0)