WA YA FI KOWA KARYA A CIKIN HALITTUN ALLAH ?



WA YA FI KOWA KARYA A CIKIN HALITTUN ALLAH ?
:
*TAMBAYA*❓
:
Don Allah malam a cikin kungiyoyin gaba daya wadanda ake dangantawa da musulunci wadanne ne suka fi kirkiro abubuwan da ba su da alaka da musulunci, don su kare akidarsu ?
:
*AMSA*👇
:
To dan'uwa gaba daya a cikin kungiyoyin musulunci babu wadanda suka fi 'yan shi'a karya, da kirkire-kirkire marasa asali, ga abin da daya daga cikin magabata yake cewa :
Ma'abota ilimi da masu hankali sun cimma daidaito cewa : 'yan shi'a sune kungiyar da suka fi kowa karya, kuma karyarsu dadaddiya ce, wannan ya sa malaman hadisi suke banbance su daga mutane saboda yawan karyar su, ga maganganun wasu daga cikinsu :
Abuhatim Arrazy yana cewa : "An tambayi Malik game da rafidha (Yan shi'a) sai ya ce : "Kar ku yi Magana da su, kar kuma ku yi riwaya daga gare su, saboda suna karya"
Imamush Shafi'i yana cewa " Ban taba ganin wadanda su ka fi iya shaidar zurr ba, kamar Rafidha"
Sharik kuma yana cewa : "Ina daukar ilimi daga duk wanda na hadu da shi amma ban da 'yan shi'a, saboda suna yiwa Annabi s.a.w. karya"

Duk wanda ya jarraba su, zai gane tsananin karyarsu, ta yaya zuciya za ta amince da wanda karyarsa ta yi yawa ?.
Duba Minhaaj 2\467
 
Dr Jamilu Zarewa 

Ku kasance damu cikin wannan group domin ilimintarwa, Fadakarwa da Tunatarwa a Sunnah.
TELEGRAM:👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
FACEBOOK👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
WHATSAPP👇 
https://wa.me/+2348087788208

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚَ
Post a Comment (0)