MATSAYIN AHALUL BAITI A WAJEN AHALUS SUNNA

MATSAYIN AHALUL BAITI A WAJEN AHALUS SUNNA 


Ahalus Sunna suna É—aukar Ahalul Baiti a matsayin Musulmi na gari, masu baiwa da É—aukaka, waÉ—anda Allah ya zaÉ“e su, ya keÉ“ance su da falala da baiwa saboda kusancinsu da Annabi(SAW). Saboda haka suna girmama su irin girman da ya cancance su a Shari’a, ba tare da azarÉ“aÉ“i ko wuce gona da iri ba, kuma suna Æ™aunar su saboda sonsu son Annabi ne, kuma son Annabi son Allah ne.  
WaÉ—anda suke a cikinsu Sahabbai ne, kamar Ali da FaÉ—ima da Hassan da Hussaini da Aisha da Hafsa da Abbas da É—ansa Abdullahi, da Ja’afar da AÆ™ilu da sauransu, to waÉ—annan suna ba su daraja biyu: kasancewarsu Sahabbai kuma kasancewarsu Ahalul Baiti. WaÉ—anda kuma ba Sahabbai ba ne, ba su rayu tare da Annabi ba, kamar sauran Æ´aÆ´an FaÉ—ima Æ™anana RuÆ™ayya da Ummu Kulthum, da sauran Æ´aÆ´an Ali waÉ—anda ya haifa da wasu matan nasa dabam, irin su Muhammad binul Hanafiyya da Æ´an uwansa, da sauran zuri’o’in baffanin Annabi (SAW) da Æ´an uwansa: zuri’ar Abbas, zuri’ar Hamza, zuri’ar AÆ™ilu, zuri’ar Ja’afar, da sauransu, to waÉ—annan ana ba su darajarsu da Allah ya ba su ta kusanci ga Annabi (SAW) da haÉ—a dangantakar jini da shi. Haka nan kuma, Ahalus Sunna suna yin salati ga Ahalul Baiti tare da Annabi (SAW) a duk sa’ad da suka yi masa salati.  

Ahalus Sunna suna son Ahalul Baiti so irin na Musulunci, so na Shari’a, ba so na jahiliyya ba. Saboda haka, ba sa wuce makaÉ—i da rawa a wajen Æ™aunar su da girmama su. Ba sa dangana musu almarori, ko su Æ™udure cewa suna da wani kayan gado na annabta wanda suka keÉ“anta da shi koma bayan sauran Musulmi, ko su ce sun san gaibu, ko kuma su kaÉ—ai suka cancanci khilafa, da sauran irin waÉ—annan Æ™udure-Æ™udure na masu addini da jahilci ko son zuciya. A wajen mu’amala da Ahalul Baiti, Ahalus Sunna suna tsayawa a kan koyarwar AlÆ™ur’ani da Sunna, ba sa wucewa ko taÆ™i É—aya.   
 
HaƙƙoÆ™in Ahalul Baiti a kan Musulmi 
 
Ahalus Sunna suna Æ™udure cewa, Ahalul Baiti Allah ya Æ™ara musu yarda baki É—aya, suna da haƙƙoÆ™i a kan ko wane Musulmi waÉ—anda yake wajibi ne a kiyaye da su, kuma a bayar da su ta fuskar da ta kamata. WaÉ—an nan haƙƙoÆ™i sun haÉ—a da: 

1.    Ƙaunar su da jiÉ“intar su da ba su girma, saboda faÉ—in Allah MaÉ—aukaki, “Ka ce (ya Muhammad): Ba na tambayar ku wata ijara a kansa (iyar da aike), face dai soyayya ta cikin zumunta.” (Suratush Shura: 23) Ibnu Kathir ya bayyana cewa, daga cikin ma’anonin ayar tana nufin, “Ku so ni ta hanyar son makusantana. Watau ku kyautata musu.” Kuma ya dangana ruwayar haka ga Imam Bukhari. [Duba Tafsiru Ibni Kathir na Abul Fida Isma’il binu Kathir, bugun Maktabatus Safa, AlÆ™ahira, 1423/2002, mujalladi na 7, shafi na 123].

2.    Yin salati a gare su tare da Annabi(SAW), watau haÉ—awa da su a salati duk sa’ad da aka yi masa. Kuma ana iya yin salati ga É—ayansu yayin da aka ambace shi shi kaÉ—ai. 

3.    Ba su kaso daga khumusi (watau kashi É—aya bisa biyar) na ganima, saboda faÉ—in Allah MaÉ—aukaki, “Kuma ku sani cewa, abin da kuka sami ganima daga wani abu, to, lalle ne Allah yana da humusinsa kuma don Manzo, kuma saboda masu zumunta.” (Suratul Anfali: 41) Ibnu Kathir ya ce malamai masu yawa suna ganin kason masu zumunta ana ba da shi ga Banu Hashim da Banul MuÉ—É—alib. [Duba Tafsiru Ibni Kathir, mujalladi na 4, shafi na 37].

4.    Ƙuduri mai Æ™arfi da cewa nasabar Annabi(SAW) ita ce mafi É—aukakar nasaba, kuma danginsa su ne mafi darajar dangi. 

5.    Kare su da tsare mutuncinsu da kuÉ“utar da su daga Æ™arerayin da aka laÆ™a musu a bisa jahilci ko son zuciya. Misali irin Æ™arerayin da malaman Shi’a suke laÆ™a musu na abubuwan da suka saÉ“a da abinda kakansu, Manzon Allah (SAW), ya zo da shi na haske da shiriya dake cikin Ƙur’ani da Sunnah. 

Muhimmyar FaÉ—akarwa: WaÉ—an nan haƙƙoÆ™i da aka ambata suna tabbata da sharuÉ—É—a biyu: Musulunci da tabbatar nasaba. Watau mutum sai nasabarsa ta tabbata cewa ya haÉ—a jini da Annabi(SAW), kuma ya karÉ“i Musulunci sa’an nan yake cancantar waÉ—an nan haƙƙoÆ™i.                



•••═══ ༻✿༺═══ •••
 - *JERIN LITTAFAN SHI’A* NA 5: "Ahalul Baiti a mahangar Ƴan Shi’a da Ahalus Sunna" - na Prof. Umar LabÉ—o

✍ AnnasihaTv

Call/WhatsApp: 08142286718
Post a Comment (0)