ZAN AURI KANWAR MATAR MAHAIFINA KO YA HALATTA?

*_ZAN AURI KANWAR MATAR MAHAIFINA, KO YA HALATTA?_* *Tambaya* Malam ya halata mahaifina ya aure mace ,ni kuma na auri kanwarta. *Amsa:* To dan'uwa ya halatta ka aureta, saboda ba ta cikin mataye guda goma sha biyar wadanda Allah ya haramta a aure su a cikin suratunnisa'ai, ga shi kuma babu wani hadisin da ya haramta a aure ta, Allah yana cewa a cikin suratunnisa'i aya ta: 24, bayan ya ambaci matan da aka haramta a aura, "Duk matan da ba wadannan ba, to an halatta muku ku aure su. Allah ne mafi sani 10\3\2015 Amsawa:-Dr. Jamilu Zarewa. Gabatarwa:- ÃbûbäkÃ¥r Êkâ. Ya kai dan uwa mai Albarka ka taya mu yada wannan karatu/sako zaka samu lada mai yawa, domin yada ilimi yana da daga cikin Abubuwan da suke kusan ta bawa ga Mahalicci. ______________________________________ » Zauren 🔑 *_MIFTAHUL ILMI_* 🔑 (WhatsApp). ‎Ga ma su sha'awar shiga Zauren MIFTAHUL ILMI a whatsApp sai a turo da CIKAKKEN SUNA zuwa ga lambar mu (07036073248) ta ‎whatsApp.
Post a Comment (0)