UKU-BALA'I 35

UKU-BALA'I

NA

KAMALA MINNA

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*

​​WÉ› ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucÉ‘tÉ›, MѳtiѵɑtÉ› ɑɳɗ ɛɳtɛʀtÉ‘iɳ ѳuÊ€ ʀɛɑɗɛʀร​.

BABI NA TALATIN DA BIYAR.

Numfashin ta take ji yana fizga kamar zai bar jikinta wani irin juwa da jiri taji tana kwasarta kamar zata watsar da ita kasa idanuwanta sun ya cak! waje ko juyawa ba sayi sosai take dubansa da kallo na mamaki da wani irin yanayi zuciyarta take ji tana bugawa da duk wani jan numfashin ta kamshin take ji yana dokar mata hancinta wani irin yanayi wanda ya haifarwa jikinta da wani irin kasalallan yanayi jikinta take ji yana narkewa kamar ruwa kafafuwanta sai ƙarƙarwa suke yi suna kokarin zubda ita kasa.
Juyar da take ji tana wani irin juyawa da ita kamar wacce take samar gajimare runtse idanuwanta tayi a daidai lokacin da ta hango wasu abubuwa sun fito daga idanuwansa sun dire ana kamar saukar KIBIYAR AJALI lokaci guda zuciyata ta buga da wani irin yanayi mai girman gaske.
Sosai taji zuciyarta na buÉ—e a wani killataccen waje wanda ya jima kargame da katon kwado makullin sa ita kanta ba ta san inda ta jefashi ba sosai ta ji zuciyarta ta sauya bugu da wani al'amari mai girman gaske.
Ganin komai take yi tamkar a mafarki ba a zahiri ba ganin komai ta ke yi kamar ba a duniyar zahiri yake faruwa ba magudanan jinin jikinta take ji sun sauya a wani mataki wanda ita kanta ba zata ce gashi ba kwanyarta ta shiga kai kawo da wasu lamari masu yawan gaske wanda ta jima da binne su a zuciyarta.
A hankali take buÉ—e idanuwanta hancinta na sake dauko mata daddar kamshin sa wanda yayi matukar tasiri wajan juyar mata da duk wani kamshi da ta taba ji a filin duniyar nan.
Da sauri ta shiga warware dan-kwalin da ke kanta jikinta sai kyarma yake yi idanuwanta akansa har yanzu zuciyarta ba ta gama yarda da cewa shi ne ba sosai take ganin komai tamkar a mafarki dan yatsanta guda ta daga tana mai nuna shi bakinta na wani irin É“ari kamar wacce ruwan sama yayi wa dan banzan duka take rawar sanyi.
Shikam! mutuwar tsaye yayi zuciyarsa na bugawa da wani irin yanayi sosai yake yajin sa a sama duniyar na kai kawo dashi komai yake ji na kwanyarsa na wargajewa zuciyarsa na buÉ—e wani makeken fili tana dasa wata bishiya mai girman gaske wacce tayi rassa a lokaci guda duk ta mamaye kafatanin filin zuciyarsa.
Murmushi yake saki wanda shi akaran kasa bai san yanayi ba idanuwansa na juyawa da wani lamari mai girman gaske sosai idanuwansa suke bin Mariya da kallo kafun ya kau da kai cikin yanayin na bugun zuciyarsa da yake ji kamar zata tarwatse.
A hankali yashiga kokarin saita kansa yana jan numfashi mai taurin gaske kirjinsa yake ji yana nauyi sosai da wani abu mai girma gaske a hankali ya runtse idanuwansa.
"Yah Dr.Karami".
Mariya ta furta da wani irin sauti a muryarta wacce bata sam ma tana dashi ba bata san ta yi amfani dashi ba sosai take kallonsa sosai take jin jikinta na ansa wasu sakonni masu narkar mata da zuciya su hargitsa mata tunani.
Murmushi yayi kafun wani abu da ya tsaya masa azuciya ya wuce bayan ya haÉ—eshi dakyar.
Sautin muryarta da yaji yana ansa kuwwa a kunnuwansa hakan ba karamin narkar masa da jiki yayi ba gabadaya ji yayi sautin yana bin jikinsa yana ansa kuwwa a kwanyarsa da wani irin yanayi mai girman gaske.
"Mariya".
Ya fadi zuciyarsa na wani irin zillo kamar zata faso kirji ta yo waje.
"Yaa Allah Mariya wai da gaske kece?".
Ya sake fadi da wani murmushi mai kama da son fashewa da kuka idanuwansa naa kara narkewa da wani irin ruwa kamar na Rose tsakiyar kwayar idanunsa wani haske mai kama da na kibiya yake fitowa da sauri-sauri yana isa ga Mariya da ta gama narkewa cikin wani hali zuciyarta na wanzar da wani farinciki mara musaltuwa ji take yi kamar ta daka tsalle ta isa wajansa ta rungumeshu duniyar take ji tana sauyawa da duk wani hali da take ciki duniyar take ji tana kamfato mata wani farinciki tana ajje mata runtse idanu tayi jin abin da yace da sauri ta juya wajan da su Umma suke wayam! ta ga wajan ba kowa wata ajiyar zuciya tayi kafin taja kafa cikin sauri ko wani sashi na jikinta sai kaÉ—awa yake yi musamman kugunta da kirjinta. kafafuwanta kawai zaka kalla ka gane a harÉ—e suke tafiyar take yi amma ji take yi kamar zata kifa.
Fakare yayi da baki fuskarsa da wani kayataccen murmushi mai girman gaske idanuwansa kawai yake yawatawa akanta mamaki ne da tu'ajibi suka cika shi har yanzu zuciyarsa bata gasgata masa wai Mariya bace gani yake yi kamar wata halittace daban a tsaye a gabansa take yi masa magana gani yake yi kamar wata daban ce take tafiya a yanzu ba Mariya da yasani shekaru hudu baya ba komai ya sauya komai nata ya canza muryarta kirar jiki ta yanayin tafiyarta...
"Yaa Allah".
Ya furta yana kai hannayensa yana muttsuka idanuwansa da yake zaton karya suke yi masa gizo suke yi masa da wata mace ba Mariya ba zuciyarta na kara gasgatawa amma shi yaki AMANNA dan yatsarsa daya ya saka cikin baki yana cizawa da karfi jin zafin ya sanya shi sakin kara mai dan sauti.
"Ouchhh!!".
Ya furta yana yarfar dan yatsar nashi.
Ko da Mariya ta shiga dakin Umma na zaune tana karasa kwabin Cake din bango ta jingina dashi tana mai da numfashi da sauri-sauri idanuwanta a lumshe fuskarsa nayi mata yawo a idanuwanta murmushisa idanuwansa kai gabadaya ma fuskarsa take ganin tana kai kawo a cikin runtsantsun idanuwanta zuciyarta na wata irin harbawa da wani irin yanayi mai girman gaske numfashi ta ja kafun ta buÉ—e idanuwanta a saitin Umma da tayi mata fakare tana kallon Ikon Allah wai akace in kana da sauran numfashi kana DA SAURAN KALLO a filin duniyar nan mamaki ne ya cikata lokaci guda da taga canzawar Mariya yanayi da take kallon fuskarta da yanayin da jikin nata ya nuna wanda a tsayon lokaci mai yawa bata ga haka ba ta mance rabon da ta ga Mariya a haka bazama ta iya tunawa ba.
"Ke wai lafiyarki kuwa?".
Umma ta fadi tana mai tsuke fuska cike da mamakin Mariya tun lokacin da ta lura da shigowar Dr.Karami da yanayin da ta ga Mariya a ciki shiyasa ta zare jiki ta yo cikin dakin don ta lura tsaf! Mariya zata yi abin da zai tasa ta ji kunya a gabansa bata iya ƙewar mutum ba sam!
A duk lokacin da ta ga wani wanda suka jima ba su hadu ba ta dinga É“arin jiki kenan amma na yau ya bambanta da sauran lokuta.
Wani murmushi mai kwari ne ya kufcewa Mariya kafun ta kai hannayenta tana toshe bakinta har zuwa lokacin jikinta bai daina É“ari ba.
"Yah Dr.Karami ne fa".
Uwar harara ta watsa mata kafin ta ja tsaki.
"Eh na san shine ai shiyasa na ga sai É“arin jiki kike kamar wata sakarya ke a tunanin ki hakan da kikayi burgewa ce kina 'ya mace ki barin jiki ai sai ya dauke ki ba ki da natsuwa duk na ga abin da ya faru wanda sam bai dace ace ke a karan kan ki kike haka ba".
Zaro idanu waje tayi jin abin da Umma ta fadi da sauri ta sauya fuska alamun damuwa zame jiki tayi ta zauna kasa don jin kafafuwanta take yi kamar ba za su dauke ba.
"Au! zama kikayi ki bar shi a tsaye a tsakar gidan so kike yi ya lura da wautarki".
Runtse idanu tayi zuciyarta na wata irin harɓawa da sauri ta mike tana kokarin ficewa amma ta kasa sai kai kawo take yi tana susar kai Umma na lura da yanayin ta da sauri ta mike ta shiga kintsa dakin duk da ba wata gyara yake bukata ba komai tsaf yake hijab dinta ta dauko ta saka kafin ta dubi Mu'azzam da yake ta kasumar Cake sannan ta dubi Mariya.
"Ki dai kintsa ko".
Ta fadi fuskarta a daure kasa Mariya tayi da kai kafun ta gyara daurin dan kwallinta ta dauko hijab ta saka ita ma gabanta har lokacin bai daina bugawa ba fargaba kawai take yi ji takeyi kamar in ta fita ba zata ganshi ba gani take yi kamar a mafarki ne.
Numfashi ta ja kafun ta runtse idanu ta buÉ—e addu'a tayi domin samun sauki a zuciyarta.
A hankali taka ta fice daga cikin dakin kanta a kasa har yanzu yana nan tsaye harɗe da hannayesa a kirji dago kanta tayi ta dubesa idanuwansu suka sarƙewa waje daya lokaci guda zuciyoyinsu suka buga a tare da sauri tayi kasa da kai ganin wani murmushi da ya saki da ya kusan tafiya da imaninta.
"Sannu da zuwa Umma tace ka shigo daga ciki".
Ta fadi a wahale kafun ta juya tana kokarin komawa dakin.
"Bana son gaisuwar ai ni ba wajanki na zo ba".
Dr.Karami ya fadi da rashin wasa a muryarsa cak! ta tsaya da tafiyar da takeyi zuciyarta tayi mata wani wawan bugu ta runtse idanu kafun ta juyo cikin tsuke fuska da gayyato juriya ta ajjewa kanta zuciyarta na tuno mata da abin da ya faru na halin ko in kula da ya nuna a kanta tsayin shekaru sosai zuciyarta ta fara dauko laifinsa duk da dai bai taka kara ya karaya ba.
"Nima ai ba don halin ka na yi ba".
Ta fadi tana mai hanzarin barin wajan ta fada cikin dakin.
Murmushi yake saki yana mai nuna ta da hannu mamaki kamar ya kashe shi wai Mariya ce take magana haka ita ce tayi baki haka Mariyar da ya sani acan baya mai shiru-shiru magana ma wuya take yi mata wai ita ce da mai da masa da magana da yanayin fushi take yi dashi sai da ya gama shan sharafin mamakinsa sannan ya taka zuwa dakin a daidai lokacin ita kuma Mariya ta fito hannunta dauke da Jug na roba saura kadan suyi gware da sauri ta kauce ko kallonsa ba tayi ba fuskarta ba yabo ba fallasa yana kokarin mataa magana tayi masa wani kallo da ya sanyashi sauri sakin murmushi yana mai shigea dakin bakin sa dauke da sallama.
Bayansa tabi da kallo kafin ta ajje Jug din tayi hanyar waje kankara ta sayo ta zo ta hada masa lemo mai kayan kamshi da yake Umma na ajje kayan kamshi da kayan jinja saboda irin wannan yanayi na bako idon kunya sosai ta hada lemon sai kamshi yake yi sannan ta farfasa kankara ta saka a ciki sai da ta bashi kamar minti daya sannan ta dauka domin kai masa fuskarta a gimtse sai ka rantse bata taba yin dariya ba murya can kasar makoshi tayi sallama ta shiga idanuwansa kuwa na saitin kofar tana shiga da idanuwansa ta fara cin karo da sauri ta dauke kanta ta isa garesa ta ajje a gabansa ta mike wani plat ta dauko ta zubo masa Cake ta zo ta ajje masa duk kanta na kasa ta ki kallonsa amma shi duk motsinta na idonsa hanyar waje tayi tana kokarin fita.
"Mariya!".
Umma ta kira da wani sauti na tuhuma da sauri ta juyo ta dubeta alamu tayi mata da ido aiko sai ta kara tsuke fuska tana turo baki gaba ta gefen ido ta kalli Dr.Karami ya dauki Jug din lemon yana sha amma idanuwansa na kanta da sauri ta fice daga cikin dakin.
******
Duban Baseera tayi a dan hargitse idanuwanta ta bude su sosai kafun ta watsa mata wani kallo.
"Ke fa tsiyata dake wauta yasin daga fada miki magana kina kokarin canza mani manufa ta daban...".
Wayar dake hannun Baseera ta daura Ringing da sauri ta duba lokaci guda ta balle da dariya tana duban Mariya da tayi fakare da idanuwanta kallo daya zakayi mata ka gane ba cikin hayyacin take ba.
"Ke My Besty Mutumin ne fa yasin...".
Duka ta kai mata kafun ta mike tana kokarin ficewa a daidai lokacin ita kuma Baseera ta daga tana ansawa ganin Baseera na kokarin fita tayi sauri dauke wayar daga kunnanta.
"Billahillazi yana kofar gida ya biyo ki".
a firgice Mariya ta juya tana dubanta Baseera dake faman kwasar dariya idanuwanta a warwaje lokaci guda suka kaÉ—a kamar za tayi kuka.
"Yo ni mai ya dame shi dashi ai ba waje na ya zo ba...".
Da sauri Baseera ta mike tana katse wayar da dariya a bakinta.
"Yasin Karya kike daga gidan Umma yake yana nemanki Umma ta fada masa kika na nan yarinya kin gudu baki tsira bane bari ki ga".
Baseera ta mike tana zarar mayafinta tana kokarin fita waje ganin haka ya sanya Mariya saurin riketa.
"Ke fa ba hankali kika cika b ina kuma zaki kin san Allah ko kin je kin ce ina gidan ba zan fita ba domin kuwa ba abin da zan masa".
Tagumi Baseera tayi da hannu daya kafun ta saki wata dariya.
"Uhmm wai ma ni wallahi dariya kike bani mutumin nan yau satin sa kusan biyu yana zarya akan ki yana baki hakuri akan abin da yayi miki amma ke kamar wata dutse gabadaya kin kasa bashi lokacinki Mariya karki mance fa waye Dr.Karami karki mance lokacin da kika saka ni gaba akan baya kula ki ya manta dake amma yanzu dama ta samu kina kokarin sakinta".
Haushi ne ya turnuke Mariya tayi sauri ta fizge jikinta daga Baseera ta koma bakin gado ta zauna ta na mai zabga tagumi fuskar nan a haÉ—e kamar hadari da sauri Baseera ta iso gareta tana mai dafa mata kafada.
"Yi hakuri mutuniyar tashi don Allah muje bai da ace mutum kamar Dr.Karami kina yi masa haka ba...".
"Don Allah ki rabu dani Baseera karki saka raina ya bace kisan Allah ba zan fita ba ai in na fita kamar bani da zuciya ne".
Zaro idanu tayi waje kafun ta shiga dubanta sosai ganimn take yi kamar ba Mariya ba komai take ganin ya canza game da ita fushin da ba nata ba take ganin Mariya ta aro ta daurawa kanta akan mutumin da sam bai dace ace tayi wa haka abin yayi matukar daure mata kai don haka sai ta koma gefe tana mai latsa wayarta ta ba banza ajiyar Mariya.
******
Da sauri ta sauka a Napep din ta nufi hanyar shiga gida ko gabanta bata kallo idanuwanta gabadaya a rufe suke ba zato ba tsammani taji tayi karo da mutum da sauri ta dago kanta ta na fiddo su waje cikin yanayi na tsoro da firgita tsuke fuska tayi ganin wanda yake gabanta da sauri ta kau ce tana kokarin wucewa cikin gida caraf! taji ya rike mata hannu ai ji tayi kamar ta kurma ihu wani kallo ta watsa masa kafun ta fizge hannun nata rai bace ta shiga nuna sa da yatsa.
"Huzaif kana da hankali kuwa kasan abin da kake aikatawa hannu na fa kari ke...".
Wani kallo da yayi mata yana kokarin sake riketa da sauri ta ja baya kafun ta daga hannu ta zabga masa mari cikin tsananin takaici da bakin ciki.
"An gaya maka ni irin watsantsun matan da kasani ne an gayamaka RA'AYINMU DAYA da su ne ko an gaya maka halayarmu daya da su ne tun wuri ka dawo hayyacin ka in kuma ba haka ba na rantse da Allah zan yi maka abin da baka taba zato ba".
Murmushi ya saki yana yawatawa da idanuwansa a jikinta kafun ya shiga kokarin kaiwa gareta a hankali ta shiga ja daya baya idanuwanta a warwaje cikin tsananin tsoro da firgita yanayin da ta ga Huzaif a ciki ya tabbata mata ba ya cikin hankalinsa da sauri ta juya tana kokarin kwasa da guda sautin karar marin da taji ya karaÉ—e kunnuwanta ne ya sanyata tsayawa cak! kafin ta juya a firgice.
"Dr.Karami!".
Ta fadi a firgice jikinta har rawa yake yi wani irin huci yake yi kamar kumurci yana faman cika fuskarsa ta rine tayi jajir idanuwansa sun kaÉ—a sosai hannusa akan Huzaif da ya dafe kuncin sa domin kuwa sosai yaji shigar marin da Dr.Karami yayi masa kallon kallo suka shiga yi wa juna a tsakanin su sosai suka so tuna in da suka san junansu.
Dr.Karami ya ja numfashi mai zafi kafun ya dubi Mariya da tayi matukar shiga firgice kamar wacce zata saki fitsari ba abin da jikinta yake yi sai rawa sosai ta tsorata da yanayin da taga Dr.Karami a ciki musamman irin kallon da taga yana watsa mata kau da kai tayi tana kokarin barin wajan wata irin razananniyar tsawa ya doka mata lokaci guda ta tsaya da tserewar da take kokarin yi a hankali ya shiga takowa inda yake gabanta na dokawa da tashin hankali mai girman gaske nuna ta yayi da yatsa bakin sa sai motsi yake yi yana son yin magana amma ya kasa ya dunkule hannu ya naushi iska yana mai cizon laɓɓansa kafin ya juya ya kalli Huzaif da har lokacin yake tsaye dafe da kuncin sa karasawa yayi gareshi yana kallonsa ido cikin idon kafin ya ja huci mai zafi.
"In har kasa sake gangancin ka ya sake dibarka har kayi kokarin taba ko da gyalan jikinta ne na rantse maka da Allah sai na daureka har igiya tayi rara don na lura kuruciya na damun kwanyarka zan saita maka ita".
A hansale Huzaif ya dube shi.
"kan wannan kucakar yarinya ka mare ni kan wannan mai kama da birin ka mare...".
Ji kake kau! Dr.Karami ya sake dauke shi da mari wanda yafi na dazu ya cakumi wuyar rigarsa.
"wai kan dan gidan uban wanene fada min uban waye uban ka a garin nan na rantse da Allah in bakayi wasa ba kafatanin zuri'arku sai sun ji a jikinsu".
Yana gama fadin haka ya watsar dashi gefe kafun ya dubi in da Mariya take cikin tsananin firgice da razana bata yi zaton zafin Dr.Karami ya kai har haka ba sosai taji tsoronsa ya sami ma sauki a zuciyarta kasa tayi da kai ganin wani kallo da ya watsa mata mai cike da tuhuma zuciyarta taji tayi wani irin dokawa da hanzari ya isa can gefen hanya in da yayi parking lokacin da ya ga abin da ke faruwa tsakanin Mariya da Huzaif a hanzarce ya isa yayi mata ki ya fizge ta cikin tsananin bacin rai huci kawai yake yi zuciyarsa na wani irin zafi da raÉ—aÉ—i ji yake kamar ya hada Huzaif din da Mariya yayi musa dan banzan duka.
Sai da taga bacewarsa sannan ta juya ta dubi Huzaifa tana mai galla masa harara tayi hanyar shiga cikin gida a soro ta ci karo da Hafsat tana kokarin fitowa taci uban kwalliya da dinkin atamfa wanda yayi matukar kama mata jiki ainun in ka ganta sai ka rantse wata rikakkiyar wayayyice nan kuwa kanta empty ne a hankali take taku Mariya na binta da kallon mamaki da tu'aji bi da yarda Hafsat ta bari duniya ta buÉ—e mata ido haka ko da yake bata ga laifin ta ba Goggo Marka ce ta daure mata kugun yin abin da take so tun da suka hadu da Huzaif shikenan ta daina zaman gida kullum yana hanyar daukar ta suna ficewa ita dai nata ido domin bazata taba mance cin amanar da Huzaif da ita kanta Hafsat din sukayi mata ba kallon su kawai take yi girgiza kai tayi tana mai shigewa cikin gida zuciyarta a jagule komai take jin ya kwance mata duniyar gabadaya tayi mata zafi ji take yi kamar ba ita ba.
"Kan Uban can!".
Hafsat ta fadi lokacin da taga Huzaif na faman huci hannunsa dafe da kuncin sa idanuwansa sun kaÉ—a sun yi jajir kamar wanda kayi wa sura ce da barkono.
"Me ya same ka haka?".
Ta fadi tana mai duban sa, tsaki ya ja kafun ya shiga safa da marwa a wajan sai fama huci yake yi.
"wani dan iska ne wai don kawai waccan yarinyar ta gidan ku za ta gaya min ba dadi shine ya zo ya daura min tafi a fuska".
Zaro ido tayi waje kafun ta dubi kofar gidan su.
"Mariya ko?".
"to akwai wata yarinya ce a gidan ku bayan ita".
Ya fadi a hassale kamar zai kifeta da mari ita ma tsaki ta ja tana mai galla masa harara.
"Huzaif na lura so kake yi ka raina min hankali in ba don haka ba ina ruwanka da ita ai ko me akayi maka kai ka ja yasin".
Wani wawan cafka ya kai wa hannunta ya murÉ—e ta saki kara mai sautin.
"Ni zaki raina wa hankali Hafsat kin san Allah in bakiyi wasa ba sai na sauke akan ki".
"Sauke mana in ka isa ai bani na saka ka kula ta ba Malam balle ka sauke fushin ka akai na".
Dunkule hannu yayi kamar zai kai mata naushi amma sai ya bugi iska gami da jan tsaki ya isa in da yayi parking ya buÉ—e mota ya shiga ransa a bace zuciyarsa sai faman tururi take da takaici
Hafsat dake tsaye ganin yarda ya shiga motar rai bace ba tare da yayi mata magana ba haushi ya cika ta ja tsaki kafin ta isa gareshi kallonsa kawai tayi ta watsar kafun ta buÉ—e motar ta shiga ko kula ta bai yi ba ya yiwa motar Key ya fizge ta ya bar layin yana mai fadin.
"Billahillazi sai na baiwa Mariya mamaki ba dai ni ta saka akayi wa cin mutuncin ba zan nuna mata na fita iya shege".
Hafsat da ta kula tsaki taja a ranta tana fadin 'Allah ya kara ai ni nafin son haka dama kiyayya mai karfi ta ratsa tsakaninku'...

*_KAMALA MINNA_*😘😘😘
Post a Comment (0)