UKU-BALA'I 53

UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​.

BABI NA HAMSIN DA UKU.
 *_My Kawa Amra ina tayaki murnar kammala labarin ki mai taken AMRAH NAKE SO Allah ya amfani al'umma da ilmin da kika nuna a ciki da fadakarwa ya kara miki basira da hazaka....Makarantar Uku bala'i yasin laifin Amrah ne da kuka jini shiru 2days kurciya tayi mani_*😁
  *_Milk Candy Happy Bizday Allah ya karo shekaru masu amfani ya inganta rayuwa sai mun zo cin Cake_*😁😁😁
haka kawai taji zuciyarta na tashi kamar wanda taci abun da ranta bai so ba tunda aka kawo ta cikin gidan Dr.Erena gabadaya ta rasa gane kanta sosai take jin zuciyarta na raɗaɗi da zafi ga wani kunci mai girma da take jin yana ta faman kai kawo a ko ina na zuciyarta da ruhinta.
 Numfashi take faman saukewa kamar wacce tayi gudun fanfalaki a hankali ta sauko daga kan gadon jikinta sanye da wando da riga wanda suka kamata sosai bayan su ga rigar barci da ta sanya a sama sannan ta daura zani akai duk wannan abin da tayi ta yi ne saboda kar Dr.Erena ya shigo mata daki duk da ta kargame da key amma duk hakan bai kwantar mata da hankali ba barci ma gagararta yayi a hankali ta shiga takawa har ta isa toilat din tayi abin da zata yi ta fito haka kawai take ji wani iri gabadaya ga wani kamshi da take shaka yana tayar mata da zuciya tun ranar da aka kawota gidannan take jin haka amma ta rasa dalili isa kofar dakin tayi ta buɗe da key sannan ta leka ganin ba kowa ya sanyata sakin ajiyar zuciya ta nufi F
falon gidan a hankali tana dube dube cikin yanayi na dan tsoro don bazata manta arangamar da tayi da Dr.Erena aa a daren ta na farko inda suka kwashi rigima tun ranar bata haduwa dashi ba sai dai taji shigowarsa da fitarsa amma ko sau daya bata taba gangancin fitowa yana gida ba.
 Tunda ta tunkaro falon take jin warin na daɗuwa sosai har sai da ta toshe hancinta sosai ta shiga zare idanu gabanta na tsananta bugawa yawatawa da idanuwanta ta shiga yi cikin falon amma bata ga kowa ba hakan ya bata mamaki matuka cikin yanayi na tsoro da fargaba ta tsaya tsakiyar falon tana dube dube sam bata lura da mutumin dake kwance saman kujera ba bata san ya taso ba sai dai kawai taji an danko mata kugu wata irin razananniyar kara ta saki tare da toshe hancinta da take jin warin ya dadu nan ta shiga kiciniyar kwatar kanta amma ina rikon da yayi mata ba na wasa bane ji tayi kamar zata mutu numfashinta sai faman fizga yake yi runtse idanu tayi gami da yin wani yinkuri sosai taji karfi ya zo mata wanda bata san tana dashi ba ta fizge kanta ta daka tsalle can gefe guda sai faman numfarfashi take yi.
 Kallo ta bishi dashi da idanuwanta da suka gama razana da tsoro sosai ta firgita da yanayinsa gani take kamar ba Dr.Erena da ta sani ba gabadaya ya canza suffarsa take ganin tana riketa mata kamar ba nashi ba da sauri-sauri ta shiga ja da baya kafun lokaci guda ta kwasa da gudu tayi dakinta ta mai da kofa ta rufe zamewa tayi ta zauna jikin kofar ta runtse idanu cikin wani irin yanayi zuciyarta sai zillo take yi kamar zata faso kirjinta ta fito.
Ta dauki lokaci mai tsayi a wajan zuciyarta da kwanyarta sai kai kawo suke yi mamaki take yi yarda take jin warin nan da ya jima tana jinsa bata taba zaton a jikinsa yake ba sai yau Allah kawai ya kwaceta amma ta tabbata in ba don haka ba da tuni ta mutu don sosai take jin warin na ratsa mata hanci yana samun masauki a cikinta.
Wani kuka ta saki mai ciwo ita kam! taga ta kanta ba ta san kaddarar da ta jayota wannan gidan ba bata san mai yasa tayi wannan AUREN ƘADDARA din ba ita kam bata ga amfanin wannan auren gareta ba illa bala'i da zai jaza mata.
*****
Abu kamar wasa Gabadaya Areefa ta rasa gane kanta tun ranar da wannan lamarin ya faru tsakaninta da Dr.Erena sosai ta firgita yau kimanin wataninta biyu kenan a gidansa amma ta rasa kwamciyar hankali da natsuwa.
 "Maama don Girman Allah ki zo ki fiddo ni daga cikin wannan gidan zan mutu".
Cewar Areefa a wani talatin dare da tayi wani mugun mafarki da yayi matukar tsorata ta.
 "Wai me ke damunki ne Areefa eyee ba na ce miki ina nan zuwa ba amma kin ki kwatar da hankalinki ki natsu mana ina nan zuwa gobe da safe".
Wani kuka ta sake rushewa dashi matsanancin sai faman zarya take yi a tsakiyar dakin daga ita sai kayan barci kanta duk a hargitse kamar sabuwar mahaukaci.
 "Allah Maama mutuwa zanyi ba zan iya jira har gobe da safe ba don Allah ki zo ki fiddo ni daga bakin gidan nan...".
Bata karasa maganar da take yi ba taji an hau dukar kofar dakin nata kamar za a karyata wani tsalle tayi ta ɗane saman gado idanu a warwaje.
 "Maama kina ji ko kin gan shi nan fa ya zo yana dukar min kofa wayyo Allah na zai kashe ni".
 "Innalillahi wa inna ilaihr raji'un".
Hajiya Layla ta fadi cikin sauti don tana jiyo sautin bugun kofar da ake yi sosai ta firgita ita kanta ta fara tsorata da yanayin da take jin Areefa a ciki sosai take fargarbar abin da zai je ya dawo kai kawo kawai take yi tsakiyar falon tun lokacin da Areefa ta bugo mata waya tana kuka gabadaya ta fice hayyacinta bata son abin da zai cutar da Areefa bata so a kuma yin na biyu bata so ace ta dalilinta Areefa take fadawa cikin kunci da bala'in rayuwa.
Hannayenta ta saka ta dafe kanta tana jin yarda yake juya mata a hankali ta ja kafafuwanta da take jin sun yi mata nauyi sosai ta zauna bakin kujera jikinta sosai yake rawa.
 "Areefa kina jina".
Ta fadi cikin kwantacciyar murya mai cike da rarrashi.
 "Ina jinki Maama ni dai don Allah ki zo ki fidda ni daga cikin gidan nan na roke ki".
Ta fadi tana mai sake rushewa da kuka a daidai lokacin kuma ya balla kofar ya shigo habawa ba ta san lokacin da tayi cilli da wayar ba ta yi hanyar toilet da gudu tana shiga ta mai da kofa ta rufe.
 "Areefa!!".
Taji ya ambaci sunanta cikin wata murya wacce ta tabbatar bata sa bane gabadaya sautin ta ya cika mata kunnuwa yake yi kamar gidan ma rawa yake yi gabadaya lokaci guda ta sake rikicewa sosai.
Kara kankame jikinta tayi sosai idanuwanta a runtse ba abinda take ambata sai sunayen Allah hawaye sai faman sauka suke a kuncita zuciyarta na kara rikicewa.
  A kunnuwanta take jin taku wanda yake ansawa a dukkanin bangwayen gidan ko ta ina kasa da sama zubewa tayi ta zauna kasa cikin yanayi na yanke tsammani abin da yake kokarin faruwa da ita.
 Bata san mai ya kai ta yarda da auren nan ba, bata san wani tsautsayi bane yasaka ta amincewa dashi, tana cikin bala'i. wanda bata san ya za ta fidda kanta ba tsoro take kar abin yayi yawa ga duka ga mari gami da tsinka jaka.
Wasu hawaye masu zafi suka zubo mata daidai lokacin da taji takun kafafuwansa na takowa zuwa toilet din fargabarta ta dadu da sauri ta shiga ja da baya domin kafafuwanta take jin suna kokarin kasa daukarta handle din kofar da aka rike hakan ne ya sanyata dauke numfashi gabadaya na dan lokaci kafun ta ji an saki a juya kuma an fara tafiya a hankali jin shirun da tayi na ɗan lokaci ya sanyata sakin gwauron numfashi tana dafe kanta da yake faman sarawa kamar zai rabe gida biyu numfashi take fizga zuciyarta na kara rikicewa da wannan lamarin wanda bata san yarda zata kwatantashi ba.
 Haka ta cigaba da zama cikin wannan talatin daren har zuwa wani lokaci wanda ita akaran kanta ba zata iya cewa wani lokaci ta dauka ba domin barci a lokacin bata san ina ya nufa ba idanuwanta sun kekeshe kiran sallar assalatu ne ya fargar da ita daga duniyar tunanin da ta lulaka cikin kasalallan yanayi ta mike tana jan kafafuwanta da take jin su kamar zata zubda ita kasa ta isa wajan famfon Toilet bayan ta yi tsarki ta daura alwala zuciyarta na ta nazarin ta yarda zata fice daga dakin don gabadaya ta gama firgicewa bata san abin da zai faru ba in ta fita daga toilet din nan bata so ta hadu dashi ta tsane shi sosai take jin tsanarsa na kara samun gurbi a zuciyarta sosai take ganin wautar kanta da ta yarda har ta amince akayi wannan auren gashi yanzu tana cizon yatsa.
 Sai da ta gama tsalle tsalle da zuciyarta kafun ta tunkari kofar jikinta na faman bari ta buɗe kadan ta leka ganin ba kowa a hankali ta shiga takawa ta fito ganin tabbacin ba kowa ta karasa kusa da kofar ta mai da ta kulle gami da sargafa key wani irin numfashi ta ja gami da jingina da kofar ta runtse idanuwanta zuwa wani lokaci kafun ta buɗe ta ja kafafuwanta sallaya ta dauko ta shimfiɗa gami da saka hijab ta shiga bada nafilfili zuwa wani lokaci tana kai kukanta wajan Allah ya rabata da wannan mugun mutumin ya tsare mata rayuwa ya kare ta sosai take zubda hawaye zuciyarta na kara karaya da tashin hankalin rayuwar da take ciki a yanzu faragaba take bata san abin da zai faru ba tana tsoron abun da zai faru ya hada har da ita shiyasa tun farko ta so Maama ta fada mata komai da zai faru da ita a wannan gidan domin ta shirya amma bata yi haka ba ga shi yanzu tana ganin bala'i....
Ringing din wayar tace ya katse mata dogon tunanin da ta zauna tana ta faman yi bayan ta sallame da gudu ta mike don har ta tsoro amma jin wayarta ne ya hakan ya sanyata shiga dubanta in da ta cillar da ita jiya can ta jiyo sautin bayan loka din gadon ta da hanzari ta isa ta rarumo ta ganin Maama ne ya hakan ya sanyata sauri daga kiran muryarta na rawa.
 "Maama kin taho ne kina ina yanzu?".
Ta fadi da ɓarin jiki numfashi Hajiya Layla ta ajje jin muryar Areefa alamu ya nuna ba abin da ya same ta.
 "Areefa dafatan dai kina lafiya ba abin da same ki?".
 "Ni dai kawai ki taho Maama don Allah ki zo ki fiddo ni daga cikin gidan nan...".
Da sauri Hajiya Layla ta tare ta.
 "Ba maganar zuwana Areefa in har na zo Dr.Erena zai gane ke wacece kuma zai gane ni kin ga kuwa in ya san waye ke ai da matsala...".
 "A,a Maama ni ba damuwa ta ba ce ya san ko ni wacece in har zan fice daga cikin gidan ba zan iya zama ba ki zo ki cece ni".
Ta karashe muryarta na kara karyewa da kuka sosai durkushewa tayi a wajan jin Hajiya Layla ta ce ba za ta zo ba kenan duk abin da zai faru da ita sai dai ya faru kenan.
 "Areefa".
Hajiya Layla ta fadi amma Areefa bata ansa ta ba sake kiranta tayi nan ma bata ansa ta ba sai ma kashe wayar da tayi ta cillar da ita kan gado zuciyarta ta shiga hasaso mata wani lamari mai girma wanda take kokwanto akan sa tsakaninta da Hajiya Layla tana SHAKKA akan kalaman da take furta mata tana shakka anya ba yaudararta tayi ba domin wani kudiri nata anya kuwa ba GADAR ZARE ta saƙa mata ba ta rufta ciki.
Girgiza kai ta shiga yi kamar wata kadangaruwa cikin tsayin lokaci kafun ta mike tana kai kawo cikin falon da matsanancin tashin hankali mai girman gaske sosai take jin zuciyarta na son gasgata abin da take sanar da ita sosai take jin girman lamarin a ko ina na sashin jikinta.
Bata son hasashenta ya tabbata bata son maganar zuciyarta ya zama gaskiya tana tsoro akan abin da zai je ya dawo in har hasashenta ya tabbata to tabbas da matsala wanda bata san ya zata fuske ce ta ba.
Zame jikinta tayi ta zauna bakin gadon hadi da zabga tagumi zuciyarta da kwanyarta sai faman hayaniya suke yi suna kokarin kamawa da wuta domin gabadaya ji takeyi komai ya rikice mata ta kasa samun tunanin da zata yi.
Ihu taji gami da tsayuwar mota a lokaci guda bata san lokacin da ta zabura ba tana kokarin kwasa da gudu tayi hanyar bayi taja tunga ta tsaya tana faman rarraba idanu bata san gari yayi haske haka ba daga kai tayi daidai inda agogon dakin yake karfe bakwai har da minti hamsin 7:50 mamaki hakan tayi domin bata san lokacin ya ja haka ba nan tsaye take tana jiyo sautin ihun nata shi yana kusantowa cikin gidan sosai daidai lokacin da ka buɗe kofar falon aka shigo ta tsinkayo faduwar abu mai karar gaske har sai da ta sanya hannu ta toshe kunnuwanta gami da runtse idanunta...
 *_KAMALA MINNA_*😘
Post a Comment (0)