UKU-BALA'I 59

UKU BALA'I
           NA.
    KAMALA MINNA.

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​.
  BABI NA HAMSIN DA TARA
Runtse idanu tayi daidai lokacin da ya isa inda take tsaye kwankwarar motsi ta kasa yi zuciyarta sai faman harbawa take yi kamar zata faso kirji ta fito waje kwanyarta take ji tana yawo dauke da wani irin hayaniya mai kama da saukar a radu buɗe idanunta tayi a karo na ba adadi ta sauke a saitin inda fuskarsa take sai faman sauke mata wani shu'umammen murmushi yake yi wanda yake kara rikita mata duk wani tunani nata da natsuwarta.
Bata san ya za tayi ba zuciyarta gabadaya ta gama tafiya a duniyar Dr.karami lokaci mai tsayi tayi kokarin kwatar kanta amma abin ya ci turo sai ma abin da ya cigaba sosai take jin zuciyarta na kara matsewa da kaunarsa kaunar da take jin ta tana kara hayayyafar 'ya'ya wanda ba za ta iya cewa ga adadin su ba kaunar ce zallarta ba tare da hadi ba wanda ta jima da AMANNA akan haka kaunar Dr.Karami kamar halitta ce da Allah yayi mata tun lokacin da zai busa mata numfashi.
Wani numfashi ta sake ja a daidai lokacin da taji takunsa na kusantowa gareta yana kara sautin bugun zuciyarta ko wani sashi na jikinta take jin yana narkewa kafafuwanta jin su take yi kamar ba za su dauke taba.
 "Mariya!!!".
Ya fadi da wani irin sautin da ya sanyata sumar tsaye gami da sadakarwa zuciyarta ta tarwatse da sautin zazzakar muryarsa mai dauke da wani sirrin mai kokarin fallasa sirrin dake boye a bayan zuciyarta.
Buɗe bakinta tayi ta shiga kokarin buɗewa domin ansawa amma hakan ya gagara sai ma motsi da laɓɓanta suke yi amma ta kasa furta wata kalma wacce zata taimaka mata domin dawowa hayyacinta.
Idanuwansa ne suka sarke cikin nata a bazata wanda hakan ya sagar mata da duk wata gaɓa ta jikinta wanda za ta taimaka mata wajan kwatar kanta daga barin kallonsa wani maganakisu take hangowa yana zabarin duk wani sirrin dake cikin idanuwansa yana sarkewa da nata.
Wani yin kuri tayi mai tafe da numfashi ta kau da kanta tana faman ajiyar zuciya wani murmushi ne mai girman gaske ya bayyana akan k'yank'yawar fuskarta sai faman kaɗa kwayar idanuwanta take yi.
Ba zato ko tsammani taga mutum ya durkushe a gabanta da sauri tayi kokarin ja baya amma sai taji kamar an kafe mata kafafu ne dago idanuwansa yayi ya sauke a saitin nata tare da kokarin kamo hannunta guda wanda ta rufe rabin fuskarta dashi.
 "Ina son ki Mariya zuciyata ta gama gajiwa so ne kawai a cikin ta yake zarge ko wani sashi da loko na cikin ta GURBIN SO da na baki wanda ya kasance ke kadai ce a cikin sa so nake yi ki bani damar da zan farfaɗo dashi daga sumar da yayi na wucin gani kice dani kina so na zan zamo ABOKIN RAYUWA a gareki".
'Yaa Rabbi!!".
Ta fadi cikin bugun zuciya kankame jikinta tashiga yi domin ta rasa me zata yi ta rasa ma a wata duniyar take a wannan halin ta kasa sarrafa kanta gani take yi kamar ba ita ba gani take yi kamar wata Mariyar ce ba ita ba wai Dr.Karami akan gwuiwowin sa yana neman SO gareta shine yake fada mata kalaman da suke kokarin tarwatsa mata zuciya da kwanya ba zata iya ganin sa a haka ba ba zata iya sakin kunnuwanta taji kalaman da yake fadi kanta yayi kadan ya dauka komai zai iya faruwa zuciyarta zata iya fashewa da kaunarsa kaunar da take hangota tafi duk wata kauna da masoya suke nuna wa junansu.
Bata taba zaton zata tsinci kanta a wannan matakin ba bata taba zaton zuciyarta zata iya sakewa haka ba har ta saurari irin wannan kalaman...
 "Ki ce wani abu mana duniyar nan a yanzu mu kadai ne a cikinta karki bari kunya tayi miki SAGEGEDUWA ki fito fili ba wanda zai ganki ki kalle ni a matsayin ni kadai ne babu kowa ki kalle ni a a matsayin wanda shine a matsayin ABOKIN RAYUWA a gareki".
'Anya kuwa'.
Ta fadi cikin zuciyarta da k'yar.
Dan yatsarta na tsakiya taji ya kama gabadaya ji tayi wani irin Shock ya kamata duk wata kofar dake jikinta runtse idanu tayi tana mai jan numfashi kamar zata shiɗe da sauri ta shiga ambaton 'Yaa Ilahi!'. Kafun ta shiga kokarin kwatar kanta amma ina shigar zobe da taji cikin dan yatsar nata ne ya sanyata sakin jiki sosai ji da tayi ya sakar mata hannu ya sanyata ja da baya da sauri tana mai da numfashi buɗe idanuwanta tayi saitin hannunta da take ji kamar ba nata ba duban hannun nata tayi wani hadadden Zobe ta gani sai k'yalli yake yi ruwan Gold mai tsananin kyau da burgewa sosai taji wani iri a zuciyarta da saurin ta dube shi shima ita yake duba idanuwansa sun yi wani kala kamar ruwan Rose sai sheki suke yi.
"Please My Pretty Say something to me?".
Ya fadi da wata kwantacciyar murya wacce zata iya rantsewa ba tasa bane in ba don ta ganshi a gabanta ba sannan laɓɓansa na motsawa cikin wani irin salo wanda yake kara rikita mata tunanin kwanyarta.
Hannun ta dago mai zobe a ciki ta shiga kallon zoben tana tabawa da dayan hannun nata wasu abubuwa taji kamar sako suna shiga jikinta a duk sa'ilin da ta murza zoben harufan dake jiki suke kara sanyata jin wani iri kyallin da suke a tare ne suke kara sanya zuciyarta son zoben.
"Duniyar nan ina so ta zamo tamu mu kadai ki dubi duk girman ta da fadin ta ki saka a ranki mu kadai ne a ciki ba wani wanda zai fado cikin ta har ya so ba mu wata matsala".
Dam! taji gabanta ya bugu jin furucin sa zuciyarta ne ta mikata wani mataki mai girma da nisa 'Dr.Aqeel' zuciyarta ta bankado mata runtse idanu tayi sosai wani sashi ya shiga kawo mata shi tana kara kamba mashi a gareta kai ta shiga girgizawa a hankali wasu hawaye suka tarun mata a GURBIN IDO bata so ba bata so abin da zai kara rikita mata rayuwa a irin wannan lokacin mai girman gaske a gareta tashin hankali take tsoro bata so a sake komawa gidan jiya so take yi duniyar ace ta cigaba da wanzuwa a wannan matakin da take ciki a yanzu amma bata tunanin haka zata kasance dole ta hakura dole ne...
"Kuka!!!".
Ta ji muryarsa kamar an hura sarewa gabadaya taji kunnuwanta sun dauka kwanyarta ta dau sautin sosai ji tayi tana yawo kamar zata zube a kasa.
"Mariya kukan me kike yi haka...fada min please ko na ɓata miki rai ne?".
Yanayin yarda yake maganar ya kara narkar mata da zuciya a tausayin sa ta sani tana son sa amma bata san yarda zatayi da Dr.Aqeel ba shima yayi mata HALACCI bata so ace ita tayi masa BUTULCI girgiza kai ta shiga yi.
'Ba yarda zaki yi dole ki zaɓi daya don mace bata auren NAMIJI sama da daya'.
Zuciyarta ta fadi mata hannayenta ta saka ta rufe kunnuwanta ji take yi kamar furucin zuciyarta da take kamar a bayyane yake.
'Dr.Aqeel'.
Ta fadi a zuciyarta sai dai abin da bata sani ba shine maganar da tayi a bayyana take.
Dr.Karami da ya tunkaro wajanta don rarrashi jin abin da tace ya sanya shi saurin jar burki yana mai watsa mata wani irin kallo mai cike da tuhuma da zargi lokaci guda ya ji zuciyarsa na harbawa da sauri-sauri runtse idanunsa yayi sannan ya buɗe akanta.
Ita kanta a jikin ta taji yarda kallon nasa ke ɓulata hakan ya tabbatar mata akwai abin da tayi wanda ya sanya shi yi mata irin wannan kallon dago idanun ta tayi ta dube shi da sauri ta kau da kanta zuciyarta tayi wani irin dokawa.
 "Mariya da gaske kike abin da najiyewa kunnuwa na gaskiya ne?".
Ya fadi muryarsa da zafi a cikinta wani iri taji jikinta nayi mata sosai ta gano laifin don haka da sauri ta shiga girgiza kai zuciyarta na rikicewa da tashin hankalin da ta hango a idanunsa sosai taji kanta na cakuɗewa yana mikata wani mataki wanda bata taba jin ta a cikin sa ba.
 "Karki ce mani shine kar ki ce mani zuciyarki na gareshi karki ce mani shine mai GURBIN SO a zuciyarki bani ba don Allah Mariya na roke ki karki buɗe bakin ki ki sanar da ni gaskiya ne na san karya kunnuwa suka jiye mani Please Don't say anything".
Ya karashe cikin jarumtar zuciyarsa da yake jinta kamar zata tarwatse numfashi yake ja a hankali da sauri ya daga hannayensa duk biyun ya dafe kan sa da su wani irin juyawa yake jin kansa nayi kamar zai tarwatse gida biyu.
 Laɓɓanta ta tura cikin bakin ta tana cizawa kuskuren da take ji tayi take son ya zama a mafarki ba gaske ba ba za ta iya cigaba da kallon Dr.Karami a yarda take ganinnsa a yanzu cikin wani irin yanayi da take jin yana karta mata zuciya.
 "kai ne...".
Ta fadi da kyar zuciyarta na yinkurawa kamar zata tarwatse hakan ya hanata karasa abin da tayi niyyar fadi.
 "Ni ne me Mariya fadi nine me don Alalh ki bude bakinki ki fadi naji ko zuciyar tawa zata rangwanta min daga ciwon da ta tsomani a ciki.
 Juyawa tayi da sauri tana kokarin barin wajan da sauri ya riko mata hannu ya matse sosai har sai da tayi kara mai dan sauti dubanta yake yi cikin idanunta da suka kaɗa sukayi jajir.
 "Ba zan sake ki ba har sai kin fada min matsayi na".
 "Ina son ka Dr.Karami kai ne mallakin zuciyata..amma ka sani ina tsoron butulci...".
A hankali ya sassauta mata rikon da yayi mata wani murmushi na bayyana a saman fuskarsa ya shiga girgiza kai.
 "ba a so dole sannan kyautatawa daban so shima daban karki ce don Dr.Aqeel ya taimaka miki a rayuwa haka na nufin sai kin so shi a,a ban ce karki so shi ba amma ba wai wanda zai cutar dake ba ki ajje batun sa a gefe ki anshi SO na mu rayu tare".
Girgiza kai take yi a hankali tana dauke hawayen da suke zubo mata maganar tasa take jin ta wani iri a zuciyarta da kwanyarta laɓɓanta ta shiga motsawa alamun son yin magana amma ta kasa sai murza zoben hannunta take yi.
 "Mariya!!".
Ya ambata cikin wani irin yanayi mai tafe da mamaki da al'ajabi da sauri ta dube shi ganin yana kallon kofar gidan su ya sanya itama ta juya da sauri ware idanu tayi waje ganin Hafsat ta leko ko mayafi babu ga turtsetsen ciki a gabanta runtse idanu tayi kafun ta dubeshi zuciyarta na dokawa da sauri-sauri.
 Kallon tuhuma yake yi musu su dukan biyun kafun ya ja numfashi ya dubi Mariya wacce itama izuwa wannan lokacin ta dawo da dubanta gareshi kwalla ne suka kawowa idanuwanta farmaki da sauri ta hadiye su.
 "Me kenan Mariya me ke faruwa ne da Hafsat haka karki ce mani...".
Shiru yayi cikin yanayin tausayi yana girgiza kai don ya tabbatar da zarginsa ganin yarda Mariya ta rikice.
 "Allah ya kyauta".
 ya sake fadi ganin Mariya bata da niyar cewa komai sake kallon Hafsat yayi wacce itama a daidai wannan lokacin idanuwanta na kansa kau da kai yayi cikin faduwar gaba da sauri ya juya ya koma cikin motarsa wata katuwar leda ya fiddo da ita ya ajje gaban Mariya kafin ya juya da sauri ya koma cikin motarsa zuciyarsa nayi masa zafi sosai.
Sakin baki tayi tana kallonsa har ya ja motar bayan ya dago mata hannu ya wuce sannan ta sungumi ledar jiki a sanyaye tayi hanyar gida har zuwa lokacin Hafsat na tsaye bakin kofar ko motsi ba tayi ba.
 "Haba don Allah Hafsat haka da kike yi fa wallahi bai dace ba zubda mutunci ne kike yi duk wanda ya ganki a haka dole yayi miki wani kallo na daban".
Gyatsi ne tayi kafun ta kalli hannun Mariya ta kau da kai.
 "Meye naki a ciki ko kina tsoron kar Dr.Karami yayi zargin duk daya ne".
 'Allah yayi min tsari da aikata mugun abu irin wannan'.
Mariya ta fadi da sauri cikin zuciyarta gami da raɓa Hafsat tayi shigewarta cikin gida zuciyarta da takaicin halin Hafsat duk da abinda ya faru da ita amma har yanzu ba za tayi karatun ta natsu ba ta saita rayuwarta sosai take jin bakin ciki da takaicin halin da Hafsat ta tsinci kanta sosai abin ke taba mata zuciya amma ita Hafsat ta kasa fahimtar ta na daukar da take yi mata na 'yar uwa ciki daya...
*Kamala Minna*
😍😍😍
Post a Comment (0)