UKU-BALA'I 73

UKU BALA'I
   NA.
    KAMALA MINNA.

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​.
  BABI NA SABA'IN DA UKU

 *MARUFI...*
"Mai Ciki".
Kamar daga sama taji sautin muryar Bassera na fadin haka, cikin dariya a hankali ta mike tana gyara doguwar rigar dake jikinta, ta taka hankali ta nufi kofar fuskar da murmushi, Handle din ta rike gami da buɗewa.
Baseera ce tsaye, hannunta sarke da na Dr.Aqeel hankalinsa gabadaya na wajan wayar da yake yi sai ɗan ta TAUFEEQ dake sagale a kafaɗar Dr.Aqeel din.
 Numfashi Mariya ta ja kafun ta zaro idanu waje, da sauri ta koma ciki tana mai kwalawa Dr.karami kira, da yake kicin. Wai yana yi mata wainar fulawa tunda ta tashi take kwadayinta shi kuwa ya zage sai yayi bayan kuma tace zata aikawa Umma tayi mata, yace bai amince ba shi ma ya iya.
 Da sauri ya fito idanuwansa sun yi jajir, hannunsa rike da cokali fuskar gefe guda duk Manja, bata san lokacin da ta kwashe da dariya ba ta shiga nuna masa kofar shigowa falon tana yi masa alama da baki amma ya kasa gane wa, sai ma harara da wurga mata yana fadin.
 "Ni ko ai ko ba za ki ci wainar nan ba tun da abin ya zama haka...".
Bai karasa ba Baseera ta bayyana cikin falon, duban su tayi kafun ta sauke idanuwanta a saitin Dr.Ƙarami da yayi wiki-wiki dashi.
 "Iyee ba shakka, likita kai ne haka".
Ta fadi tana kwashewa da dariya, a sa'ilin da Dr.Aqeel ya sanyo kai shima yana kokarin sauke TAUFEEQ a kafaɗarsa, ganin abin da ke faruwa ya sanya shi isa cikin falon da sauri ya kwantar da Taufeeq da ya yi barci ya zauna gami da zabga tagumi yana kallon Dr.Karami, kafun lokaci guda ya kwashe da dariya.
 "Aboki ashe kai ma kuku ka zama tabbas arzuki yaci uban na da, an sai da gida an sai yashi".
Gabadayan su suka kwashe da dariya, kafun Dr.Karami ya juya da sauri ya fada kicin, yana tuntsirar dariya shima.
 "Billahillazi baki da M matar nan yanzu Doctor guda ya zama kukun ki".
Baseera ta fadi tana duban Mariya, taɓe baki tayi tana mai cewa.
 "Dadin abin ai ba ni kadai ake yi wa wannan gatan ba na ga wata mike kafa take yi ta tura mijin nata kicin ya yi ta fama da cokali a hannunsa".
 "Rabu da ita Maman Jawwad yanzu haka kafun mu fito, nifa nayi girkin wai bata da lafiya ba yarda na iya haka na shiga na zabga girkin kuma saboda rashin tsoron Allah ta miki kafa ta buɗe ciki ta ci".
 Dr.Aqeel ya fadi yana marere cewa alamun ya ji jiki wani kallo Baseera tayi masa kafun ta ce dashi.
 "Au haka ma zaka ce? to shi kenan tun da kace haka da ga yau raba girki za mu din ga yi da kai, kowa ya din ga yin kwana bibbiyu".
Zaro idanu yayi gami da daura hannu aka, kamar wanda ya ga wani mugun abu ya shiga marmaɗi da idanu kamar wanda yayi wa sarki karya.
Baki Mariya ta saki ganin yarda yayi a daidai lokacin shi kuma Dr.Karami ya fito, hannunsa dauke da faranti shake da wainar fulawa taji manja ya iso gaban Mariya ya kalle ta sama da kasa kamshin wainar ta doki hancinta lokaci guda taji miyau dinta ya tsinke, da sauri ta kai hannu zata dauka ya kau ce yana yi mata gwalo gaban Dr.Aqeel ya isa ya zauna ya dube shi.
 "Wannan aikin maza, ne don haka zo mu ci a tsakaninmu, in sun yi zuciya suyi na su mugani".
 Ya fadi yana daukar waina daya ya kai bakin sa kafun ya mike ya nufi firji ya buɗe ya dauko musu gorar ruwa da ta lemo masu rangwamin sanyi.
Baseera baki ta saki kafun ta dubi Mariya dake tsaye tana ta faman hadiye yawu, fuskarta duk tayi wani iri kamar zata fashe da kuka a hankali Baseera ta mike ta dube su.
 "Dadin abin mu ba kutare bane, sannan kuma muna da hannun da za muyi bari ma ku gani".
Tana fadin haka ta mike ta nufi in da Mariya take sai faman hadiyar yawu take ta rike hannunta suka nufi Kicin.
Da gudu Dr.Karami ya mike hannunsa da waina daya gaban su ya sha ya riko hannun Mariya gami da bude mata baki, ya tura mata wainar aiko kamar jira take ta shiga taunawa har tana kokarin kwarewa.
Baya Baseera tayi tana kallon ikon Allah kafun ta juya ta dubi nata Mijin da ya dauke kai yana ta faman kai loma bakinsa.
 "IKON ALLAH"
Abin da ta fadi kenan tana rike haɓa.
*****
Karar faduwar abu ne ya sanyata fitowa daga kicin cikin sauri, sai faman jan kafa take yi da turtsetsen cikin ta tana cizon laɓɓanta daidai benen da zai kai ta sashinta kafarta ta turguɗe ta yo baya runtse idanu tayi don ta sadakar taje kasa har ta hango irin zabar da wahalar da zata sha jinta tayi jikin mutumin da bata taba zato ba, wani numfashi ta ajje a daidai lokacin da ya riko mata kugunta ya haɗe da jikinta sosai kamshin turaren sa Dark-wood wanda ya rigaya ya zama jikinsa ya daki hancinta hakan ya kara sanyata lafewa a jikinsa.
Sun dau lokaci a haka kafun ya ja numfashi bayan ya gama shinshinar kamshin da ke fita daga cikin sumar kanta da ta sha gyara ta tufketa da rumbos.
 "Kashe ni zaki yi ko Preety?".
Ya fadi yana mai dago haɓarta da hannu daya, idanuwanta a runtse suke har zuwa wannan lokacin taki buɗe su ita kadai ta san yanayin da take ciki a wannan mataki, zuciyarta take ji tana mikata wata duniya ta daban mai cike da farin ciki na tsanani kaunar da take ji zuciyarta na kara narkewa ta mijin nata abin alfaharinta.
 Iska ya shiga hura mata a idanu ta shiga motsa manyan kwayan idanuwanta ba tare da ta buɗe ba, wani murmushi na kara bayyana a saman ƙyankyawar fuskarta wacce tayi fayau ba digon ko tabo a jikinta laɓɓanta masu taushi da kalar ja sai faman motsa su take yi a hankali ta shiga buɗe idanuwanta daya bayan daya ta sauke su a saitin fuskarsa.
 "Jawwad!".
Ta fadi da wani irin sauti a muryarta kafun ta shiga kokarin mikewa daga lallausar jikin nasa da bata gajiya da kwanciya a kanshi kirjinsa da ya zame mata abin kwanciya a kullum in ba a nan ta kwanta ba ta taba jin dadi sannan ba ta iya barci.
 "Me ya yi kuma?".
Ba tace komai ba ta mike daga jikin nasa gabadaya ta kwace kanta daga rikon da yayi wa kugunta a hankali ta shiga takawa tana kokarin hawa sama amma jin yarda kugunta ya ansa ya sanyata tsayawa cak! tana mai cizon laɓɓanta.
 "wash!!!".
Da hanzari ya riko ta, yana mai duban inda ta rike.
 "Ya dai me ke damun ki haka?".
Turo bakin tayi gaba gami da taba kugun nata da take jin sa kamar zai karye.
 "Shiyasa nace maki ki dawo dakin kasa da zama amma kin ki wannan benen so yake yi ya karya min bayan mata wallahi".
Kafin ta ce wani abu caraf! ya sungume ta kamar wata Baby ya hadata da jikinsa sosai ita kuwa ta shiga kiciniyar kwace kanta amma ina rikon da yayi mata ba na wasa bane hakan yasanyata yin lamo a bayansa tana cizan masa kunne har suka isa dakinta da sauri tace dashi.
 "Don Allah sauke ni Jawwad yana ciki fa!".
"Ai baki isa ba wallahi sai na kai ki har ciki sannan na rama cizo na da kikayi mani".
Jin abin ya yace ya sanyata marere cewa tana shagwaɓe baki alamun son yi kuka hakan da yaji da sauri ya sauke ta yana riko hannunta.
 "Ai wallahi sai na rama haka kawai so kike yi ki rage mani farashi budurwa tace bata so na ko".
Zaro idanu tayi waje tana dubansa gabanta taji ya yanke ya fadi kafun ta tako kusa dashi tana zira idanuwanta cikin nasa.
 "Me kake cewa wacece gangancin da neman ciwon zuciya take so ta zama MATAR MIJINA a garin nan?".
Yanayin da ta nuna yayi matukar bashi mamaki bai hango wani razana ko tsoro a idanuwanta ba amma ya hango tsantsar so da kuma kishi na asali a cikin idanuwan nata.
 "Abin da kika ji shi na fadi".
Ya karashe yana rike Handle din kofar ya tura yana kokarin shiga ciki da sauri ta sha gabansa tana sake saka idanuwanta cikin nasa.
 "Ban hango akasin gaskiya a idanuwanka ba bai kamata kake barin harshen ka na kokarin fadin abin da ba daidai ba".
 "Injiwa ya fada miki ba gaskiya nake fadi ba ai kina sauke mani TAGWAYE na zan dakaro miki sabuwar amarya fil a leda".
Zaro idanu tayi kafun ta mai da kallonta zuwa cikinta ta shiga shafawa.
 "Tagwaye fa kace ni gaskiya a,a cikina guda daya ne kacal zan haifa ba wani tagwaye".
"Au! Wasa kika dauka to ai shikenan Allah ya kamu lokacin zaki ce na fada miki".
Ya karashe da dariya sosai a fuskarsa ya fada cikin dakin, sake da baki ya barta tana bin sa da kallo, sannan ta bin cikin nata da yayi katoto ba kamar cikin Jawwad ba gyaɗa kai ta shiga yi, a zuciyarta tana jin kamar maganar Dr.Karami gaskiya gabanta taji ya yanke ya fadi ba abin da ta tuna sai lokacin haihuwar Jawwad yarda aka sha artabu.
Wata dariya ce ta zo mata lokaci guda ta saketa da gudu ta fada cikin dakin duban Dr.Karami tayi da ya baje a gadonta can gefe kuma Jawwad ne da kwalbar Humra din ta da ya tarwatsa ta da sauri ta isa gareshi yana ganinta ya mike yana shirin gudu ta riko shi sannan ta dubi Humra din da ta kwarare a tsakar dakin sannan ta dubi Dr.Karami kara ta saki a razane ya tashi yana dubanta wani kallo ta watsa masa kafun ta turo baki gaba tana nuna masa Humra din ta dariya yayi kafun ya dubi Jawwad da yayi tsuru-tsuru.
 "Ni fa ba ruwana ke da ɗanki ne jiya nan yayi mani barna zan dake shi kika hanani don haka sai ke kiji in dadi".
Jin abin da yace yana kunshewa dariya hakan ya sanyata duban Jawwad ta talla ke masa keya ta shiga dire-dire da kafafu tana shagwaɓe fuska alamun son yin kuka.
 Da sauri ya taso ya iso gareta ya kamota ya hadata da jikinsa sosai ya sanya bakinsa saitin kunnanta yana yi mata raɗa fizge kanta tayi ta tureshi bai ankara ba yaji ya faɗa kan gadon bin shi tayi tana kokarin turmushe shi yayi sauri matsawa gabadaya ta fada kan gadon binta yayi ya danne yana mai yi mata cakulkuli dariya ta shiga yi sai da yayi mata lilis da jiki sannan ya daga ta idanuwanta a rufe sai mai da numfashi take yi kiss ya manna mata a kumatu kafun ya riko hannunta ya shiga kallonta zuciyarsa na kara buɗewa sosai a son ta GURBIN SO da ya bata a duk wani fanni na zuciyarsa yake ji yana kara buɗewa da kaunarta kaunar da har abada ba ya tunanin zai iya yiwa wata ƴa mace a filin duniyar nan.
 "INA KAUNAR KI".
Ya furta da wata irin murya da ta galabaitar da zuciyar Mariya a lokaci guda ji take yi zuciyarta na mikata wani waje na musamman mai tatttare da so da kauna zalla ta Dr Karamin ta sosai take jin zuciyar na kara buɗewa da kaunarsa sosai take jin duk bugun numfashinta na kara haifar da sabuwar kaunarsa a zuciyarta.
 "INA KAUNAR KA".
Ita ma ta fadi da wata murya da ta daki kunnuwansa runtse idanu yayi yana jin yarda bugun zuciyarsa ke karuwa saitinta yaje ya kwanta yana jawota cikinta sosai ya matse ta har sai da ta saki ƴar kara ta buɗe idanuwanta.
 "Dady kai ko".
Kamar daga sama suka jiyo muryar Jawwad na fadin haka da sauri suka dube shi don sun manta ma dashi a wajan gwalo Dr.karami yayi masa kafun ya mika masa hannu alamun ya taho da sauri yaje maimakon yaje wajan sa sai ya nufi wajan Mariya da sauri yana faɗawa jikinta.
Dukkansu ya hada ya matse a jikinsa yana furtawa Mariya kalamai zafafa da suka kara tabbatar mata da Dr.karami na tane ita kadai har gaban abada.
     KARSHE!!!.
ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH!! ALHAMDULILLAH!!!

Godiya ga Allah da ya bani ikon kammala labarin na ina godiya sosai ga maso wannan labarin da su ta jimirin bibiyata har zuwa wannan lokaci ina godiya
 Ina neman afuwanku ga dukkan wani makaranci da na batawa rai da wanda na sani da wanda ban sani ba ku sani dan adam ajizi ne.
 Ku masoya ne ba na tunanin zan yi abu da gangan don na bata muku ku ajje haka a ranku
 Yau dai mun sauke labarin Uku bala'i
Shin wani darasi kuka dauka a labarin nan?
Mai ya bata muku rai a cikinsa?
Me yafi faranta muku cikinsa?
Wani jarumai ne suka fi burge ku sannan wanne su ka bata muku rai?

Tsakanin jaruman nan me za ku iya cewa a ko wani dayan su
Kalma akan Mariya
Kalma akan Baseera
Kalma akan Dr.Ƙarami
Kalma akan Dr.Aqeel
Kalma akan Hafsat
Kalma akan Goggo Marka
Kalma akan Areefa
Kalma akan Hajiya Layla
Kalma akan Dr.Erena
Dss
Shawara ko gyara
Kofa abuɗe take
Whatsapp 08076708191
Call 07039355645
Gmail.Kamalminna217@gmail.com
Fatan alheri ga kowa da kowa ina son ku masoya sai mun hadu a sabon aiki a sabuwar shekara mai taken.....😁Sai kun ji...lolz

Post a Comment (0)