SARKIN SARAKAI BOOK 1 - 10

SARKIN SARAKAI BOOK 1. 10

GIMBIYA SHUKURA tacigaba da cewa aibazan bari ka mutu ba face na cika burina dakai ka kwantar da hankalinka ka sani cewa maigidanka sarki sahibul hairii na nan a raye bai mutuba.
Yanzun nan zan nuna maka zahiri ka gani, gama fadin haka keda wuya saitayi nuni da dan yatsanta guda izuwa jikin bango take wani irin haske ya fito daga cikin dan yatsanta ya dira a jikin bangon saiga hoton sahibul hairi kwance a sume cikin dakin nan na maridai a tsakiyar gawarwakin maridan A lokacinne ya farfado daga dogon suman da yayi ya mike ya zauna da kyar yana ta faman haki kamar zai mutu.
Ko ina a jikinsa rauni ne yai kaca kaca da jini gimbiya shukura ta dubi bawa haluf tace kaga halin da maigidanka ke ciki akwai dakuna goma sha biyu kowanne dakina dauke da masifa iri iri masifunda suke dakunan gaba sun ninka na baya yanzu ya wuce dakuna biyu saura goma a gabansa. Idan har ya wuce ta cikin ragowar dakunan goma yana raye yaci jarrabawata, don haka zan taimaka masa mu sace gatarin sihiri tare mu tafi izuwa gidan boka shamzubul Azwas dan dauko yarinya Alfila. Abinda nake soka gane shine zamu hada karfi da karfe ne domin nida shi kowa ya biya bukatarsa amma duk wannan zata farune idan ka bani hadin kai ka sadu dani yanzu' 'lokacinda haluf yaji wannan batu sai hankalinsa ya tashi fiye da ko yaushe ya rasa abinda zaice kawai saiya kurawa gimbiya shukura idanu yana mai al ajabin al amarinta . Wannan shine abinda ya faru tsakanin gimbiya shukura da bawa haluf bayan ta sa an sauya masa kamanni an shigar dashi ckin birnin askandariyya ba tareda sanin sarki barusaba ++ ++
Al'amarin jarumi uban jarumai kuwa wato sahibul hairi lokacinda ya farfado daga suman da yayi ya tsinci kansa cikin tsakiyar gawarwakin maridannan guda dubu yaga har yanzu gashi yana numfashi bai mutuba sai ya cika da mamaki kuma ya shiga tunanin zuci yace a ransa. '' wannan fa shine mataki na fardo da zanbi don biyan burina Amma gashi bani da tabbacin zan kai gaci yaushene zan samu nasarar daukar gatarin sihiri a cikin wannan gidan sarautar sannan na tafi gidan boka shamzubul azwas don dauko yarinya alfila na tabbata cewa masifar dake can fadar boka shamzubul azwas ta ninka wacce ke nan sau dubu idan ma na sami nasarar dauko Alfila yay tafiyarmu zata kasance nida sadauki Awaisu don neman wadannan 'yan matan uku wadanda zan Aura na cika burina na duniya......
Shin zamu sami nasarar ganin yan matan kuwa Alhalin babu wanda yasan a inda suke? Koda sarki sahibul hairi yazonan a tunaninsa sai yaji nadama tazo masa bisa gagarumin aikin daya daukowa kansa nan take zuciyarsa ta karaya ya fara aiyanawa a ransa cewa lallai a cikin wannan tafarki zai rasa rayuwarsa, gwarama ace ya rungumi kaddara ya zauna da talaucinsa har ajalinsa ya riskeshi... ¤ + + + + + + + ¤
SHIN BAWA HALUF ZAI AMINCE YA BIYAWA GIMBIYA SHUKURA BUKATARTA? .
SHIN SARKI SAHIBUL HAIRI ZAI IYA SHALLAKE MASIFUN DAKE CIKIN RAGOWAR WADANNAN DAKUNA GUDA GOMA? .
INA LABARIN GALADIMA AMINUL HAS WANDA SARKI SAHIBUL HAIRI YABAR MASA RIKON KASA, KUMA YA KASANCE A CIKIN TASHIN HANKALIN MAHASSADA .
marubucin yace mu hadu a SARKIN SARAKAI kashi na biyu donjin ci gaban wannan kasaitaccen labari. anan Nake cewa mu hadu a cikin littafi na biyu domin jin yadda zata kasance a wannan kasaitaccen labari nan
Zan Cigaba Insha Allah.

Post a Comment (0)