SARKIN SARAKAI BOOK 1 - 8

 SARKIN SARAKAI BOOK 1. 08

Dama tun lokacin da aka fara wannan gumurzu tsakanin sahibul Haiti da zakunan su sarku barusa Na jiyo ihunsu da gurnaninsu amma daga bisani sukaji shuru ma ana babu ihun sahibul Haiti kuma babu Na zakunan Al,amarinda ya baiwa sarki barusa mamaki kenan kawai sai ya dubi wadansu dakaru dubu uku tace maza kuje cikin wannan dakin Kasan su gano masa abindake faruwa shinn zakunann nan sunn kashee sarki sahibul hairii ko kuwa shine yakarkashesu. Yayinda dakaru sukaji wannan umarni Na sarki barusa sai hankalinsu ya dugunnzuma suka tsaya suka yi charko charko suna kallon junansu aka rasa Wanda zai wuce gaba Ba wani dalili bane yasa wadannann dakaru suka kasa zuwa wqnnan daki ba sai saboda bala,in dake cikinsa Shidai wannan wuri an tanadeshine musamman son hallaka iron mutanan da aka yankewa hukunncin kisa hakika sarrki barusaa karyaa yayiwa sahibull hairi cewaa a wannan bangareen gatarinn sihirinn yakee A cikin wannan gidaan kasa India sarki sahibul hairii ya fadaa akwai dakuna gomaa sha biyuu a cikinn kowanne dakinwl akwaii masifa iri dabann masifar dakina farko ta bata kai wacce take dakii nabiyu baa wadda ke dakin Na uku tafi ta daki nabiyu Wato dai abin bi dabi be har zuwa dakin karshe wato Na gomaa sha biyu Idan mutun ya kuskura ya fada daki Na farkoo toga babu wata hanya da zaibi ya fito dolene sai yabi ta cikin ragowar dakunaa goma sha dayann Lokacinda sarkibarusa yaga dakarunsa sunnoke sun kasa lafiya cikin wannan wuri sai ya tuntsure da dariyar far in ciki yace lallai kun Sani cewa ba a Shigaa wannan wuri a fito a rayee Ko shakka babu wannan makiyi namu tuni yanzu ya hallaka,, Koda fadawa da jama at gari sukaji wannan batu sai suka bushe da dariya nan take aka cigaba da shagali tamkarr babu wata miskila data task ++. +++. ++. ++
Al amarin sarki sahibul haiiri kuwa lokacinda yaga ya kashe zakunan nan gudaa dubu saiya fadii kasa yana haki saboda tsananin gajiyaa Visa dole ya yanke hukuncin ya tsaya yayi jinyar jikinsa kafinnan kafin ya tunkari daki Na gabaa tunda dai baisan masifar dazai iske ba a cikinta nan take ya kwance wata karamar jakaa dake kugunsa ya fiddo wani Baron magani ya shashahafa a jikinsa sannan ya kwanta a cikin gawarwakin zakunan nan son ya huta Faruwar hakan keda wuya sai bacci ya saceshi bai saniba aikuwa bai farka ba sai da rana ta fadi kodaya bude idonsa ya tsinci Kansas cikin gawarwakin zakuna kuma ya fuskancii cewaa ya Dade yana wannan bacci sai ransa ya baci domin yaso ace duk bala inda zaiyi ya dauko Gagarin sihirin a cikin abinda vai wuce ss a biyarba har yabarr kasar Askandariyya Nan take kuma sahibul haiiri yaji yanajin yunwa gashi kuma bai taho da jakar guzuri ba ya barta a can bayan gari wajan bawa haluf nanfa hankalinsa ya tashi SBD yasan cewa Indaii yacigaba da Shiva dakunan wannan gida a haka zai jya rasa rayuwarsa tunda gajiya da yunwa a jikinsa babu kuzarinda zai iya yin yaki Yana cikin wannan haline dabara ta fado masa nan take ya farke cikin zakuna ya fiddo kayan cikinsu yakama cinsu danye bataree da gashiba tunda babu wutarda zaigasa run yana yamutsa fuska SBD rashin jin dadin naman a bakinsa harma yajiyasaba da rashin dadin Bai gusheba yanacin naman harsaida yaji ya koshi sannan ya mike tsaye yasake daukar takubbansa guda biyu nan ya banke kofar dakina biyu da kafarsa ya kunnna kai ciki Da shigarsa sarki sahibul haiiri cikin dakinn Na biyu sai yayi arba da wadansu irin zagba zabgan maridai wadanda girmansu ya wuce kima da tunanin bill adama kowanne daga cikin su ya ninka sarki barusa a tsawo sai biyu hakama fadinsu da kaurinsu Dukda cewa sarki sahibul haiiri Nada dakakkiyar zuciya saida ya tsorata ainun da ganin wadannan maridai Dan ko a labaran dayasha ji baitaba jincewa akwai maridai kalan suba Wadannan maridai dai su dubu ne cif kuma kowannensu Na rike da zabgegiyar makamai guda Inda za a ajiye makamin mutum daga daga cikinsu makamin ba zai dauuku ba face antara karti majiya karfii mutum arba in Sudai wadannan maridai suna da mummunar siffa maiban tsoro tamkar dodanni kallon daga zakayiwa kirar jikinsu kasan cewa karfafane domin duk naman jikinsu a cure take tamkar an shirya mulmulallen diwatsu gashi sun Tara many an damatsa jijiyoyin kwanji hakika idan aka Tara irinsu goma zasu iya yakar babban birni suciahida yaki a cikin Rabin ss a Yayinda sarki sahibul hairi yai arba da wadannan maridai sai zuciyarsa ta karaya ya juya d baya da nufin ya koma wajan da ya fito wato dakina farko aikuwa saidaya daga cikin maridan ya zuro zungureren hannunsa ya cafkoshi yai samaa dashi ya fyada da kasa Saboda tsananon radadi da zugi saida sahibul hairi yatakarkare yaji kamar an karya Massa duk kasusuwan dake bayansaa don haka saiya kasa tashi Maridin ya daga wani faskeken gatari Dame hannunsa ya dankarawa sahibul haiiri Sara a cikii aikuwa koda gatarin ya dira akan cikin sahibul haiiri saiya kakkarye amma karfinn saran yasa cikinsa ya kulle yaji kamar zai suma Kosa faruwar haka sai mamaki ya kama maridannan gaba dayansuu saboda ganin yadda karfin gatarinsu yake yasiri a cikin duk wani .wahaluki amma yau gashi bill adama yaki yayi tasiri a jikinsa harma ya zauna lafiya bayan a tarihin Gagarin ba a taba saran wani abuba Wanda ya kasa rabewa gida biyu Aikuwa sai maridannan suka taso Masa gaba dayansu shikuma yahau maridannan da Sara da suka sukuwa suka dinga kai masaaa cafka yana gocewa Babban abinda yatayarwa da sahibul haiiri hankali shine gashidai yana saransu jikinsu nadarewa yana zubar da jini amma ko kadan basa gezau kai wani lokacima harr caka musu adduna yake a cikinsu amma da ya zaree saikaga sun cigaba sa yaki saboda taurin rai da naci iron nasu Al,amarin da ya dugunzuma hankalinsa kenan ya tabbatar da cewa indai akaci gaba da wannan gumurzu a haka izuwa wani lokaci mai tsawo zai iya gajiya su sami damar hallakashi Su kansu maridan sunsan cewa yau sun hadu da shahararren bill adama domin tinda suka wanzu a wannan wuri ba a taba jeho musu mutun ya gagaresu hallakawa a cikin dakika sittin yau gashi sun shade kusan Rabin sa a suna artabu da mutum daga kacal alhali sunsha ragargaza mutane dubu cikin kankanin lokaci Ana cikin wannan dauki ba dadi ne sahibul haiiri ya sari daga daga cikin maridan a tsakiyar kai kawai sai yaga wannan maridin ya sulale kasa ya zama gawa koda ganin haka sai murna ta kama sahibul haiiri don yagano lagonsu nan fa ya wanzu yana saransu aka suna faduwa kasa matattu Yayinda .maridan su kaga yanayi musu wannan barna suma sai suka kara kaimi wajen kokarin hallakashi maimakon koka Inda suke su cafkeshi sai suka fara kaimasa Sara da suka da bugu da naushi A wannan lokaci nefa yakin ya sauya salo domin idan suka sameshi da
Naushi saikaga kamar an cillashi daga cikin kibiya Saidai kaga yaje ya manne da jikin garu akwai lokacinda babban cikin maridan yayiwa sarki wawan naushi a ciki saiyaga sahibul haiiri a sama ya manne da rufin dakin yana aman jini amma SBD juriya irin namaza bai yarda sun cafkeahi ba sai yaci gaba da saransu aka sukaci haba da mutuwa .......
YAYINDA maridannan sukaga suna dada cigaba da mutuwa sai suka rude kuma suka firgice suka rinka kaiwa sahibul hairi mummunan sara da suka shikuwa ya wanzu yana mai zilliya da goce goce a tsakaninsu a hakanne fa suka rike kashe kansu basu saniba saida aka shafe sa a uku ana wannan dauki ba dadi sannan gaba daya maridannan suka kare wato dai suka zama gawa shikuwa sahibul hairi saiya bingire kasa a sume saboda tsananin jigata wannan shine abinda ya shiga cikin fadar sarki barusa don daukar gatarin sihiri ++
Al amarin bawa haluf kuwa lokacinda ya farka daga barci sai ya nemi ubangidansa bai ganshiba kuma baiga taguwarsa ba saiya tabbatar da cewa aikin gama ya gama wato tuni sarki sahibul hairi ya shiga cikin birnin Askandariyya nanfa hankalin sahibul hairi ya dugunzuma ya rasa abinda ke masa dadi kawai saiya zauna yana shawarwari a cikin zuciyarsa abu na farko dai shine bai san halinda sarki sahibul hairi ke ciki ba a yanzu, zata iya yiwuwa ya hallaka kuma ko yana fafatawa da cikin garin haluf ya san irinsu sarki sahibul hairi basa faduwa da wuri sai dubunnan mazaje sun fadi abin tambayar a nan shine shin har yanzu ana nan ana fafatawar ko kuwa an gama? Haluf ya tuna cewa idan fa yace zai bi sahun maigidansa kuma aka gane cewa tafiyarsu daya shima sunansa gawa nan fa hankalinsaya kara dugunzuma musamman da ya tuna cewa shifa bakin fata ne duk inda ya shiga a cikin birnin Askandariyya ansan cewa shi bawa ne donhaka kamashi za ayi kawai acigaba da bautar dashi haluf na nan zaune cikin tunanin mafita kawai sai ya hango wadansu dakaru bisa dawakai kimanin su dari uku bisa dawakai a tafe suna kewaye wani keken doki cikin firgici bawa haluf ya mike tsaye zumbur jikinsa na karkarwa yana tunanin ya gudu ko ya tsaya shidai yasan cewa wancan ayari sun hangoshi don haka ma inyace zai gudu ai bashi da mafita don zasu iya kure masa gudu bisa wannan daliline haluf ya rungumi kaddara ya tsaya cak a waje daya yana jiran karasowar ayarin inyaso kome zai faru ya faru lokacinda ayarin ya iso daf da haluf sai sukaja tunga suka tsaya cak a gabansa kawai saiyaga an bude labulen keken dokin nan take wata kyakkyawar mace ta leko da fuskarta waje sukayi arba kallo daya haluf yayiwa matar yasan cewa mai sarautace saboda irin tufafin dake jikinta da kuma sarka, da awarwaron dake jikinta matar ta kurawa bawa haluf idanu tana mai murmushi a gareshi tace yakai wannan bakin fata yaya akayi kazo wannan gari namu kuma menene dalilin da yasa ka tsaya a nan baka shiga garin ba ka sani cewa a cikin birninmu gaba daya babu bakin fata koda guda daya kasancewar mijina ya tsaneku ni kuma a duniya babu abinda nake sha awa sama da na ajiye bawa baki ina kallonsa yana min hidima sa adda bawa haluf yaji wannan tambaya saiya risina cikin biyayya yace yake wannan ma abociyar kyau kiyi sani cewa a shirye nake na baki amsar tambayoyin da kikamin amma sai idan kin yi alkawari cewa zaki shigar dani cikin birninku a boye kuma cikin sirri ba tare da sarkinku ya sani ba kuma zaki boyeni har izuwa lokacinda zan kammala abinda ya kawoni kasarku yayin da taji wannan batu saita bushe da dariya tace karka damu duk zanyi maka yadda kake so yanzu saika sanar dani sunanka bawa haluf yayi murmushi yace sunana haluf ibn bilal' kyakkyawar ta maida masa da murmushi tace nikuma sunana gimbiya SHUKURA ni ce matar sarki barusa guda daya jal a duniya koda gama fadin haka saita kira shugaban dakarun dake jagorantar wannan tafiya wani zabgegen kato mai kirar sadaukai wai shi jamhas tace dashi yakai jamhas kasan bukatata wadda na dade a kan nemanta don cikar burin rayuwata wannan bakin bawa shine zai zamo sanadin cikar burina abinda nake so dakai shine ka sanar da gaba daya jama ar dake cikin wannan ayari namu cewa duk abinda suka gani ya faru a yanzu tsakanina da wannan bawa suyi shiru da bakinsu su bar komai a cikin sirri idan kuwa sirrina ya fasu gaba dayansu zasu zama gawa jamhas yayi murmushi yace an gama ya shugabata nan take yabi dakarun gaba daya ya sanar dasu sakon gimbiya sannan ya koma izuwa wajen barorinta mata suma ya sanar dasu sa adda ya komo ga gimbiya saita sake dubansa tace kuje da haluf izuwa keken dokin barorina mata ka umarcesu da suyi masa shiga irin tamu ta mata kuma su sa masa suturar mata koda haluf yaji haka sai hankalinsa ya tashi yace a ransa yanzu shi za a mayar mace aikuwa ba za a iya batar da kamanninsa ba koda anyi masa siffar mata mutum mai natsuwa da kula zai iya ganeshi har haluf yayi nufin yaki yarda da wannan sirri sai kuma ya hakura domin bashi da wani zabi wanda yafi yabi umarnin shukura ba tare da wani bata lokaci ba jamhas yakai haluf izuwa cikin keken dokin nan ya sanar dasu bukatar gimbiya nan take sukabi umarni suka kama aiki lokacinda barori mata suka kammala aikinsu sai suka dauko babban madubi suka sa a gaban haluf ya kalli kansa a ciki nanfa haluf ya cika da tsananin mamaki domin shi kansa bai gane kansa ba dukda kasancewarsa bakin fata saiya zamo farar fata kuma ya juye......
Zan Cigaba Insha Allah
Post a Comment (0)