HIKAYAR WANI ATTAJIRI DA BAWAN SARKI


HIKAYAR WANI ATTAJIRI DA BAWAN SARKI

Daga Sadiq Tukur Gwarzo

Wannan hikaya an ciro tane daga Littafin khalila wa Dimna, wani dadadden kundin labaru masu fadakarwa wanda Masani Bipdai ya rubuta tun a zamanin mulkin Annabi Zulqarnaini.

Hikayar ta fara da cewa "A wani gari mai suna Baudamana, anyi wani attajiri mai kyauta. Babbar sana'arsa itace fatauci, inda yake siyen kayayyaki daga garizuwa gari.
Sarkin wannan gari na Baudamana inda attajiri yake yana sane da ayyukan karimci da wannan attajiri keyi ga jama'a, don haka ma ya janyo shi a jiki tare da nada shi matsayin galadima a fadarsa.
Wannan attajiri, ya kasance mai yalwar hannu. Kyautarsa ta game sarakuna da talakawa. Idan yaso, ysna iya sanyawa a tara masa talakawa yayi ta raba musu dukiya, idan kuma yaso, yana iya gayyatar manyan attajirai da sarakuna walima tare da gwangwajesu da kyaututtuka.
Rannan bikin 'yarsa ya taso, sai attajiri ya gayyaci sarkin garin da wasu manyan mutane walima a gidansa kamar yadda ya saba. Wuri yayi wuri, manyan baki duk sun zazzauna akan kujerun alfarma da aka tanadar musu. Sai kwatsam attajiri ya hango wani bawan sarki akan wata kujera wadda aka tanadarwa manyan mutane, ya harde yana shan kamshi abinsa. wannan abu saiya bakanta masa zuciya. Tun daga nesa ya daka masa tsawa, sannan ya umarci askarawansa suyi waje dashi.
Akayi taro lafiya aka gama. Ashe bawannan na Sarki yayi matukar kufula da cin mutumcin da Attajiri yayi masa, duk da shima yasan yayi kuskure. A ranar da abin ya faru ma, bai iya bacci ba. Yana ta kulla Makircin da zaiyi don daukar fansa akan attajiri.
Sai bawan ya fara rayawa a ransa "Idan da zan san hanyar da zanbi don Sarki ya wulakanta Tajirin nan, da na dauki fansa ta. To amma tayaya kaskantaccen mutum iri na zai iya daukar fansa akan mutum mai daraja irin sa?".
A karshe dai, wata dabara ta fado masa a rai.
Bayan wasu yan kwanaki, wannan bawan ya shiga dakin Sarki shara da sanyin safiya, a lokacin sarki na kan gadonsa yana bacci, amma da alamun baccin da sarki yakeyi ba mai nauyi bane.
Da bawannan ya gane haka, sai kuwa ya fara maganganu kasa-kasa shi kadai, yana cewa "Duniya da abin mamaki take, yanzu ace har Attajirin bafatake ya sami sukunin rungunar matar sarki?..ooo."
Caraf kuwa sai a kunnen sarki. Yayi firgigit ya farka, da yake mutum neshi mai kishi. Ya kalli bawan nasa fuskarsa a murtuke yace " da gaske kake? Ka taba ganin attajiri ya rungumi matata?"
Bawa ya duka gaban sarki, yace "ya shugabana, kwana biyu bana samun yin bacci, yanzu ma gyangyadi ke diba ta. Idan kajini na fadi wata magana da bata gamsar dakai ba, ka yafe ni".
Shikenan, Sarki bai sake cewa bawa uffan ba. Sai dai tunanika da suka Yawaita zagaya masa a zuciya. 'Wannan bawan nawa bashi da shamaki a gidan nan, shima wannan attajirin haka, watakila akwai abinda bawan ya hango yake tsoron fada mini'
Daga nan fa sai sarki ya cika da kishi, ya fara yanke alakokinsa da attajirin nan. Kana ma, yace da dakarunsa kada su kara barin attajiri ya shigo masa gida.
Duk abinda ake Attajiri bai sani ba, wata rana yayi niyyar zuwa kawowa Sarki wata kyauta bayan ya dawo daga fataucinsa, da yazo shiga sai masu jiran kofa sukace sam ba zai shiga ba, suka sanar masa da cewa sarki ya hana su yin haka gareshi.
Wannan abu yayi matukar girgiza attajiri. Sai ya shiga kokwanton dalilin da yasa sarki ya dauki wannan hukunci a gareshi.
Ashe bawan sarkin nan yana bisa bene, kuma duk yana hangen abinda ke faruwa. Daga can nesa ya daga murya yana cewa "kai dakaru, wannan Bafatake abin so ne ga sarki, mutum ne mai daraja, zai iya sanyawa a daure mutum ko a sakeshi kamar yadda ya sanya aka koreni a ranar da ake walima a gidansa. Ku kula da kanku, abinda ya sameni na iya samunku"..
Dajin haka, sai wannan attajiri ya gano bakin zaren. Ya daga kansa ya kalle shi, sannan yayi murmushi. Bai kara ce musu uffan ba, ya juya abinsa izuwa gida.
Attajiri yayi tunanin matakin daya kamata ya dauka. Har wata zuciyar ta shawarceshi da ya haifarwa da sarki matsala a mulkinsa kasancewar shi mutum ne da kowa keso a garin, amma sai ya tuna da cewa shi matafiyi ne, ya zaga duniya, ya san illar rikici, don haka zaman lafiya ya kamata ya nema ba tashin hankali ba.
Bayan wani lokaci sai ya aika aka kira masa wannan bawa na sarki. Yayi masa karramawa sosai da kyaututtuka, sannan ya nemi gafarar sa akan abinda yayi masa a baya.
Wannan abu ya farantawa bawan sarki rai. Har ma yake cewa attajiri " Ranka ya dade, na gafarta maka, ka girmamani, ka kuma nemi afuwa ta. Don haka zanyi kokarin juyo da hankalin sarki gareka tayadda zaku cigaba da mu'amala kamar yadda kuka saba"
Abinda akayi kenan, kashe gari da Sassafe bawa ya shiga dakin sarki shara kamar wadda akayi kwanakin baya, sai ya hau surutunsa kasa-kasa yana cewa "a'aha, muna da wawan sarki a garin nan, kalli yadda yaci kabewa ya zubar a dakinsa. Abar da ake miya amma ita yake ci.."
Nan ma dai sarki yayi wuf ya juyo gareshi, yace "kai wanne irin wawa ne, a ina kaga naci kabewa na watsar a dakin nan?"
Bawa ya fadi gaban sarki yana neman yafiya, ya bada uzurin rashin bacci ne kesashi yin gyangydi idan yana aiki kamar yadda ya bayar a baya.
Tun daga nan, sai sarki ya gane karya bawan yake fada a duk maganganunsa, sai kuma yayi da-na-sanin hukuncin daya dauka akan Attajiri ba tare da yayi bincike ba. Nan take yasa akira masa shi don ya nemi afuwar sa, ya kuma yi masa tanajin kyauta gagaruma.
Karshen hikayar kenan.
Darussa:
*Kada ka raina mutum duk kaskancinsa.
* kada kakai kanka matsayin da ba naka ba.
* kada ka rinka saurin yadda da magana tare da daukar mataki.
* kada kayi girman kai wajen neman afuwar laifin daka aikata.
Post a Comment (0)