Tambaya Ta 012


Tambaya :

Slm
Dan Allah mlm mene Hukunci wadda take karin gashi


Amsa :

Alhamdulillah wassalatu wassalamu ala Rasulillah wa'ala ahlihi wasahbihi waman walah.
Bayan haka :

Haramun ne yin ƙarin gashi , sabida faɗin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam : ( Allah ya tsinewa Mai ƙara gashi da wadda ta nemi a ƙaramata , da mai yin wushirya da wadda ta nemi ayimata.)
Bukhari ya rawaito 

Daga Jabir Radiyallahu anhu yace : ( Manzon Allah ya tsawatar akan waɗanda suke ƙara wani abu a jikin gashinsu )
Muslim ya rawaito.

Kuma koda gashinta ne Wanda ta taje idan ta ƙara ta shiga ƙarƙashin wannnan hukuncin.

Malamai Hanafiyya da Malikiyya da Shafi'iyya sunyi bayani ƙarara akan haka.

" Yin ƙarin gashi da gashin ɗan Adam haramun ne , koda kuwa mutum gashinsa ya ƙara dashi ko gashin wani" 
الفتاوى الهندية 5/358
حاشية ابن عابدين 6/372

Malam Adawiy yace : " faɗin Manzon Allah ( Allah ya tsinewa mai ƙarin gashi) yana nufin wadda take ƙara wani akan gashinta , nata ko na wani ..."
حاشية على شرح كفاية الطالب الرباني 2/459


Malam Sharwaniy yace : " koda kuwa gashinta ne da ta cire daga jikinta , ko na wani. An naƙalto daga masu sharhi yin hakan ya haramta , ..."
حاشية تحفة المحتاج 2/128

Al -Majd Ibn Taimiyya yace : " bai halatta mace ta gashinta ba , koda gashin ɗan Adam ne ko wani.."
تصحيح الفروع 1/159


Wannan haramcine tabbatacce ga kowane nau'i na mata yara da manya , buduri da masu aure .
Mata masu aure baza suyiwa mazajensu biyayya koda sun umarcesu su ƙara gashin.

Daga Nana A'isha Radiyallahu anha tace : wata mata daga cikin mutanen Madina ta aurar da ƴar'ta , sai tayi rashin lafiya , sababin rashin lafiyar gashinta ya zube , sai mahaifiyar yarinyar taje gurin Manzon Allah , tace : mijin ƴa'ta yana son gashi , zan iya ƙara mata? Sai Manzon Allah yace : Allah ya tsinewa mai ƙarin gashi.
Bukhari da Muslim ne suka rawaito wannan lafazin Muslim ne.

A lafazin Bukhari cewa yayi : matar tace : mijinta ya umarceni na ƙaramata gashi. sai Manzon Allah yace : a'a , kada ki ƙara , haƙiƙa an tsinewa masu ƙarin gashi.

Imamun Nawawiy yace : wannan hadisin yazo da bayyani a fili cikin haramcin ƙarin gashi...

A wani gurin yace : wannan hukuncine da babu banbanci cikinsa tsakanin mace mai uzuri da Amarya ko waninta.

Abinda ya dace shine asami masa harkokin gashi su bada magani insha Allah za'a dace , domin Allah bai saukar da wata cuta ba saida ya saukar da maganinta , wanda ya sani ya sani , wanda bai sani ba bai sani ba.

Wallahu Aalamu
Post a Comment (0)