*KHUƊUBAR MASJIDIS SALAFIYYA BIU BORNO STATE:*
11/RAJAB/1441-HJRY
06/MARCH/2020-MLDY
🎙️GABATARWA Abubakar BN Mustafa Biu
♦️TOPIC
_(IN BAKA KIYAYE ALLAH BA- BAZAI KIYEYEKABA)_
➖NA KASASHI GIDA 3
.
.
1️➖MUQADDIMA
Bayin ALLAH! muji tsoron ALLAH musani duk wanda yakiyaye dokokin ALLAH- ALLAH zai kiyayeshi, wanda kuma bai kiyayeshiba makomarsa a duniya mummunar rayuwace da rasa jin daɗi da jahannama a lahira,
ALLAH SW yace <<wand yakau dakai daga ambatona yanada rayuwa ta ƙunci kuma zamu tasheshi a ƙiyama makaho>>
Wannan ƙuncin rayuwar ALLAH SW yana jarrabar Kafiri da Muminine da ita, shi Mumini sai yazame masa sababin tuba,
.
.
2️➖MISALAI 5 GA KAFIRAI
.
(1) FIR'AUNA= Ya mulki dukkan MISRA ga koguna da albarkatan ƙasa da arziƙi harma alfahari yake yana cewa <<shin mulkin MISRA ba a hannuna bane kuma koramunnan suna gudana a karkashina>>➖Amma kash! yaki yakiyaye dokokin ALLAH sai yahallakar dashi a kogi,
ALLAH SW yace <<gonaki nawa suka bari da gulbi* da shuke shuke da manyan muƙamai* da ni'imominda suke kakaci acikinsa* haka duk muka gadar dasu ga bani isra'il>> [SRT DUKHAN-25-28]
.
(2) QARUN= ALLAH yabashi ɗimbin dukiya gagara ƙwaƙwalwa lissafi wanda tawagane ƙarfafa ke riƙe da mabuɗansu (QASAS-76)➖Amma kash yaki kiyaye dokokin ALLAH sai yanutsar dashi da gidansa da dukiyarsa cikin ƙarƙashin (QASAS-81)
.
(3) IBN HANY AL-ANDALUSY- Fajirin Mawaƙine yayiwa wani sarki waƙa yana cewa=
Abinda kaso zai faru ba ƙaddaraba#
Yi hukunci kaine ɗaya mai rinjaye.
Bai kiyaye dokar ALLAH a harshensaba, yana fita daga fadan sarkin sai wata muguwar cuta tabugeshi yadawo yana kwance ihun kare
.
(4) Hakama Mawaƙi ALƘARAWY ɗan Lebanon yayi isgili da Musulunci ALLAH yawulaƙantashi yamutu a banɗaki saida yayi kwanaki akaga mushen gawansa,
(4) Hakama akwanakinnan wani Mawaƙi a kano ya aibanta ANNABI SAW akan Shehinsa- sai ALLAH yahanashi kwana agidan ubansa,
.
.
3️➖MISALAI DA MUSULMAI
(1) ANNABI ADAM A/S da HAUWA'U A/S suna cikin ƙololuwar ni'ima na ALJANNA amma kash basu kiyaye dokar ALLAH ba sai yakoresu daga ALJANNA zuwa doron ƙasa cikin wahala, amma ALHMDLH sun tuba kuma yakarɓa,
(2) ALQAHIRJ Wani Sarkine cikin daular ABBASIYYA yatona manyan rijiyoyi yayita cikawa zinarai da azurfa, harma dacewa 'ya'yansa= kada kuji tsoron talauci na tanadar muku dukiyarda koda za'a rabawa kowa anan garin BAGADAZA ya ishesa zama hamshaƙin attajiri, amma kash bai kiyaye dokokin ALLAH ba sai aka masa juyin mulki aka tsiyayarda ruwan idanunsa yamakance aka karbe dukiyar aka bawa wanda yayi juyin mulkin, yadawo yana bara ababban masallacin BAGADAZA abani sadaka daga dukiyar ALLAH,
(3)BARAMIKAWA=
(4,5,6,7) SADDAM, ZAINUL ABIDUNA na TUNUSIA, GADDAFI, HASAN ALBASHIR
.
.
4️➖NATEEJA
Bayin ALLAH, Kwatsam ga cutar CORONAVIRUS, ta kukkulle gidaji, garurruka, airports, chochuna⛪ Masallatai🕌 harma umara fmda ɗawafi🕋,
إنا لله وإنا إليه راجعون
Da mutane zasuji tsoron ALLAH yadda suke tsoron CORONAVIRUS da babu cutarda zai damesu kuma da duk sun shiga ALJANNA ba hisabi ba azaba
Muyawaita istigfari da tuba da gyaran aiki, waɗanda kuma aka dawo musu da kuɗaɗensu na UMARA to suyi sadak dashi ga MARAYU, MISKINAI, FAQIRAI, GAJIYAYYU da taimakon addinin ALLAH da awassulin ALLAH YAYAYE MANA,
YA RABBANA KAYAYE MANA
YA RABBANA KAKAWAR MANA WANNAN CUTAR KASA HARAMIN MAKKA DW MADINA SUCIKA DA MASU UMARA DA MAHAJJATA CIKIN LAFIYA DA WALWALA
AMIN
_# Abubakar BN Mustafa Biu_
Daga
*MIFTAHUL ILMI*
```Ga masu sha'awar Shiga Zauren MIFTAHUL ILMI WhatsApp sai a aiko da cikakken suna ta WhatsApp zuwa ga lambar Mu 07036073248```
