TAMBAYA TA 85


Tambaya
:
Naji ance wai Namiji Musulmi zai iya auren mace Kirista, amma Mace Musulma ba zata auri Namiji Kirista ba, Shin aya ce ko hadisi ko kuma magana ce kawai?
:
Amsa:
:
Haƙiƙa Shari'ar Muslunci ta halattawa Musulmi ya auri Mace Kirista ko Bayahudiya, wannan itace Maganar mafi yawa daga cikin Malamai Ma'abota Ilimi, kuma halaccin hakan ya samo Asaline daga cikin Al-ƙur-āni faɗin Allah(ﷻ):
:
وطعام الذين أوتوا الكتاب حل لكم وطعامكم حل لهم، والمحصنات من المؤمنات والمحصنات من الذين أوتوا الكتاب من قبلكم.....سورة المائدة/5
MA'ANA:
Abincin waɗan da aka zo musu da Littafi (Yahudu da Nasara) halal ne a gare ku, haka kuma abincin ku (ku Musulmi) halal ne a gare su, Haka nan (halal ne ku auri) kamammun Mata (waɗanda basa zina) daga cikin Muminai, (Musulmai) da kuma kamammun Mata daga cikin waɗanda aka zo musu da Littafi kafinku, (Yahudu da Nasara)
:
Danhaka Malamai sukace idan Ahlul-kitabi (Kirista ko Bayahudiya) ta kasance ta kame kanta bata aikata zina, to ya halatta a aureta, duk da cewa suma Ahlul-Kitabi kafirai ne Mushrikai da Nassin Al-ƙur-ani Mai girma, to amma waccan aya ta keɓance su da wannan hukunci, danhaka su kaɗai ne Allah(ﷻ) ya halatta mana muci yankan su da abincin su kuma mu auri Matan su, shi yasa wannan halacci ya taƙaita ne kaɗai akan Ahlul-kitabi (Yahudu da Nasara), amma sauran Kafirai da suke bautar waɗansu abubuwa dabam-dabam kokuma waɗan dama basu da wani abin bauta (Majusawa) haramun ne a aure su, saboda faɗin Allah(ﷻ):
:
ولا تنكحوا المشركات حتي يؤمن، ولأمة مؤمنة خير من مشركة ولو اعجبتكم،…… (البقرة/221)
MA'ANA:
Kada ku auri Mata Mushrikai (Kafirai), domin (ku auri) Baiwa Mumina shi yafi alkhairi akan ku auri Mushrika koda kuwa kyawunta ya ƙayatar daku,……
:
Haka nan wannan Halacci ya taƙaita ne kaɗai akan Maza Musulmai, amma baya halatta ga Mace Musulma ta auri Kirista, ko kuma dukkan wani wanda ba Musulmiba:
:
Saidai abin lura anan shine, halacci ne kawai akace Musulmi ya auri Ahlul-kitabi, amma ko Matsayin Mustahabbi hakan bai kaiba, danhaka Malamai sukace idan Musulmi ya aminta da cewa wannan Matar Kirista da zai aura ba zata iya rinjayar saba yayi Ridda kokuma ta iya rinjayar
'Ya'yansa zuwa ga addinin ta to shikenan ya halatta ya aureta, danhaka ana buƙatar Mutum ya kasance yana da Ƙarfin imani dakuma ilimin addini atare dashi, sannan ya kasance niyyarsa ta yin auren itace yayi ta ƙoƙarin nuna mata addinin Musulnci har ta gane ta karɓa, to amma duk dahaka Malamai sukace barin auren su ɗin shine yafi alkhairi, Musamman ma a irin wannan zamanin datmuke cikinsa wanda galibi idan anyi irin wannan auren to Kallabi ne yake jan Rawani a madadin Rawani yaja Kallabi, abin nufi da yawa mazan sukan yi ridda ne, kuma koda Mutum yana da ƙarfin imanin da ba zata iya rinjayar sa ba, to abu ne mai sauƙi awajen ta ta iya rinjayar 'yaa'yan da suka haifa tare dashi, shi yasa Malamai sukace barinsa ɗin zaifi sa Mutum yatsira da imaninsa da kuma na 'ya'yansa, danhaka gara Mutum yaje ya nemi 'yar'uwar sa Musulma ya aura
:
※(шαʟʟαнυ-тα'αʟα α'αʟαмυ)※
:
▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂
              Daga Zaυren
             Fιƙ-нυl-Iвadaт
▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂
           Mυѕтαρнα Uѕмαи
              08032531505
▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂
Doмιɴ ѕнιɢα ѕнαғιɴмυ dαкє ғαcєвooк ѕαι αѕнιɢα wαɴɴαɴ lιɴк кαwαι αyι ""lιкє""👇🏾
:
https://m.facebook.com/fiqhul.ibadat/
Post a Comment (0)