WAƘAR GODIYA

WAƘAR GODIYA

Bismillah da sunan sarki Rabbani
Ilahu ubangijin da ya ƙage ni
Salati a gunsa manzo a gare ni
Aminullah wanda ya zo mana da addini
A yau murna nake kamar gimbiya ce ta aure ni
Saboda abin faharin da ya same ni
Mujallar Zauren Marubuta ta hore ni
Daga ƙarshe gashi kuma yau ta yaye ni
Nagode da karramawar da akai a gareni
Allahu yasa ku cika da imani
Ya taimaka muku kamar yadda kuka taimake ni
Ya yi muku gata kamar yadda ku kai a gare ni
Malamina Zaidu gwarzon zamani
Abubakar Imam ɗin wannan zamani
Allahu ya kare ka daga duk wani abu mai muni
Ka tashi ƙiyama fuskarka ta na annuri
Allahu ya saka da alheri
Ya kare ka daga dukkan wani mai sharri
Jamilu ne ko ko kace jariri
Na marubuta wanda ba ya inkari. 

©️✍🏻
 Jamilu Abdurrahman 
   (Mr. Writer) 
    +2348185819176
Haimanraees@gmail.com 

Post a Comment (0)