MATAR DA TA AURI SAMA DA NAMIJI DAYA A LAHIRA

MATAR DA TA AURI SAMA DA NAMIJI DAYA A LAHIRA
:
*TAMBAYA*❓
:
Malam matar da mijinta ya mutu, sai ta yi wani auren, shin za ta sake haduwa da na farkon a lahira, in dukkansu sun shiga aljanna, ko kuma na karshen shi ne zai zama mijinta a can ?
:
*AMSA*👇
:
To dan'uwa malamai sun yi sabani akan wannan mas'alar zuwa zantuttuka guda uku :

1. Za ta zauna da wanda ya fi kyawawan dabi'u a duniya.

2. Za'a ba ta zabi.

3. Za ta zauna da na karshensu.
Wannan maganar ta karshe ita ce mafi inganci saboda fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi cewa : "Duk matar da mijinta ya mutu, ta yi aure a bayansa, to ranar lahira za ta kasance ga na karshensu" Albani ya inganta shi a Sahihu-jamiussagir a hadisi mai lamba ta : 2704.

Wannan kuma shi ne dalilin da ya hana Ummuddarda'a aure bayan mijinta ya mutu, lokacin da Mu'awiya ya nemi ya aure ta, ta ki yarda ta aure shi, saboda tana so ta zauna da abudarda'a a lahira . duba silsilasahiha hadisi mai lamba ta : 1281
Munawy yana cewa : "Malamai suna cewa : Wannan shi ne daya daga cikin dalilan da suka sa matayan Annabi s.a.w. ba su yi aure ba bayansa, saboda Allah ya riga ya kaddara cewa : matayansa ne a aljanna" duba Faidhul-kadeer 3\151

Allah ne ma fi sani

JAMILU ZAREWA

Ku kasance damu cikin wannan group domin ilimintarwa, Fadakarwa da Tunatarwa a Sunnah.
TELEGRAM:👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
FACEBOOK👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
WHATSAPP👇 
https://wa.me/+2348087788208

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚَ
Post a Comment (0)