KHUDUBAR MASJIDIS SALAFIYYA BIU BORNO STATE



KHUDUBAR MASJIDIS SALAFIYYA BIU BORNO STATE:
 🌐 *02/RAJAB/1443-HJRY
 🌐 *04/FEBRUARY/2022-MLDY* 

🎙️ _*GABATARWA👉🏼Abubakar BN Mustafa Biu*_ 

⭕ *TOPIC👉🏼(GOGE ZUNUBBANKA DA TUBA)*

➖ *mun kasashi gida👉🏼 6️⃣*

1️⃣ *-MUQADDIMMA*
  Yaku bayin *ALLAH* Haƙika *ALLAH SW* ya halicci bayinsa kuma yasanyasu masu yawan afkawa zunubbaine sai wanda *ALLAH SW* yakuɓutar, shiyasa saboda rahamarsa yabuɗe musu ƙofar tuba da komawa gareshi, 
💡 *ALLAH SW* _<<kutuba zuwaga ALLAH dukkanku yaku muminai donku rabauta>>_ {SRT NUR-31}
💡 *ALLAH SW yace* _<<kace yaku bayina dasukayi ɓarna kada kuyanke tsammani daga rahamar ALLAH, lalle ALLAH na gafarta zunubbai dukka>>_ {SRT ZMR-53}
  Ya Matashi mai saɓon *ALLAH* meyasa bazakayi nadamar laifinkaba kuma katubaba, bakasan *ALLAH* yana farin ciki da mai saɓonda yatuba bane⁉️

2️⃣ *-YALWAR AFUWA DA GAFARAR ALLAH SW GA WANDA YATUBA*
◼️ *SHEIKH KHALID RASHID* cikin littafinsa (أنين المذنبين) yace= *ALLAH SW* yayiwa *ANNABI DAWUD* wahayi cewa- YA *DAWUD* da waɗanda suka juya mini baya zasu san yadda nake saurara musu da tausayinsu da shauƙin barin saɓonsu- da sun mutu don tsananin shauƙina kuma da gaɓoɓinsu ya kakkarye don ƙaunata, wannanfa ga wanda yajuya mini baya to meye tsammaninku ga wanda yafuskanceni⁉️

3️⃣ *-ƘISSAR WANI MAI TUBA*
◼️ *MANSUR IBN AMMAR* yace= nafita wani dare naɗauka asuba yayi ashe baiyiba, sai nazauna jikin ƙaramin wani ƙofa, sai naji sautin wani matashi daga ciki yana kuka yana cewa- da izzarka da ɗaukakanka ya *ALLAH-* saɓawanda nayima banyi son saɓani dakaiba😢 kuma badon na jahici uƙubarkaba😢 kuma badon na rainakaba😢 saidai zuciyatace ta sawwala mini❗kuma shaƙiyyancina ya galabceni❗kuma rufa min asirinda kayi mini yaruɗeni❗ *Ya ALLAH, shin wayene zai ƙwaceni daga azabarka? kuma da igiyar waye zanyi riƙo idan ka katse igiyarka? wayyo ALLAH ina baƙin cikin kwanakinda nashuɗesu a saɓawa ubangijina😢 kaicona! na tuba kuma lokaci yayi inji kunyar ubangijina😢*
  *MANSUR* yace= lokacinda naji kalamannasa daga waje sai nace👉🏼
أعوذ بالله من الشيطان الرجيم 🔳بسم الله الرحمن الرحيم 🔳يا أيها الذين آمنوا قوا أنفسكم وأهليكم نارا وقودها الناس والحجارة عليها ملائكة غلاظ شداد لا يعصون الله ما أمرهم ويفعلون ما يؤمرون🔳
nan take sai naji sautin ƙara da shure shure mai tsanani, kawai sai natashi nafice, yayinda gari yawaye sai nadawo kofar sai na tarar ana sallar jana'iza a ƙofar kuma ga wata tsohuwa na kaikawo, Na tambayeta- meyafaru? Tace= kada kasabunta mini baƙin cikina, Sai nace= ni baƙone, Sai tace= wannan ɗa nane yarasu jiya da dare yayinda wani (kada ALLAH yasaka masa da alhairi) yakaranto ayarda aka anbaci wuta cikin dare daga bayan ƙofa sai ɗannawa yayita shure shure har yamutu😥
 *MANSUR* yace= sai nace- _*INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN*_ wannan shine siffar masu tsoron *ALLAH!* Tsarki ya tabbata ga ALLAH wanda yadatarda wasu mutane zuwaga nadama da tuba! 

4️⃣ *-TUBA MAGANIN MASU DAMUWA*
  Lalle maganin matasa da dattawa masu ƙunci da damuwoyi ayau shine gudowa zuwaga *ALLAH* da kuma haɗuwa da tawagar mutanenda suka tuba suka fita daga duhun zunubbai zuwa hasken tuba kuma suka fifita Aljanna akan Wuta kuma sukayi nadaman saɓonsu, 
💡 *ALLAH SW yace* <<kugudo zuwaga ALLAH>>
💡 *ANNABI SAW* yace _"nadama tubane"_
🔳 *ƊALQU IBN HABEEB* yace= lalle haƙƙoƙin *ALLAH SW* bawa bazai iya sauƙesu dukkaba saidai yayi iya gorgodo kuma yahaɗa da tuba, ba aibi bane yin laifi- aibin shine rashin tuba da kuma dogewa da yin laifin! 

5️⃣ *-TAMBAYOYIN WANI MAI LAIFI DA AMSAR WANI MAI HIKIMA*
  Wani Mutum yazo wurin *IBRAHIM IBN AD'HAM* sai yace= ya *IBRAHIM-* Haƙiƙa na sabawa kaina da aikata zunubbai da ayyukan ashsha, kagaya mini maganganu masu zafi da zasu ratsani! Sai *IBN AD'HAM* yace= ina maka maka wa'azozi da abubuwa *5*, sai Mutumin yace= kawo na *farko👉🏼*
 *[1]- yace=* kadaina cin arziƙin *ALLAH* yayinda zaka saɓa mishi❗yace= ya hakan zai yiwu ya *IBN AD'HAM* tunda shi yake ciyarwa ba'a ciyar dashi⁉️ sai yace= abin mamaki ya zakaci arziƙinsa kuma kariƙa saɓa masa⁉️ Mutumin yace= kawo *nabiyu👉🏼*
 *[2] yace=* kada kazauna a ƙasar *ALLAH* yayinda zaka saɓa mishi❗yace= ya hakan zai yiwu ya *IBN AD'HAM* tun ƙasar nasane hakama saman nasane⁉️ sai yace= abin mamaki ya zakaci arziƙin ALLAH kazauna a ƙasarsa kuma kasaɓa masa a ƙasar tasa⁉️Mutumin yace= kawo *na uku👉🏼*
 *[3] yace=* katafi inda *ALLAH* bazai gankaba yayinda zaka saɓa mishi ❗yace= ya hakan zai yiwu alhali gyangyaɗi ko barci baya ɗaukanshi⁉️ Sai *IBN AD'HAM* yace= abin mamaki kaci arziƙinsa kazauna a ƙasarsa kuma yana gininka duk inda kake kuma kazo kana saɓa masa a idonsa⁉️ Mutumin yace= kawo *na huɗu👉🏼*
 *[4] yace=* idan Mala'ika yazo karɓan ranka kace dashi= bazan mutu yanzuba❗yace= wa zai iya hakan ya *IBRAHIM⁉️* alhali *ALLAH SW* yana cewa _<<idan ajalinsu yazo baza'a jinkirta musu sa'a guda ba kuma baza'a gaggauto musu shiba>>_ [YNS-29]⁉️Sai yace dashi= abin mamaki kaci arziƙin ALLAH kazauna a ƙasarsa kums yana ganin a ko'ina kuma bazaka iya tunkuɗe mutuwaba amma kuma kazo kana saɓa mishi⁉️ Mutumin yace= kawo *na biyar👉🏼*
 *[5] yace=* idan Mala'ikan azaba yazo yakaika wuta a ranar ƙiyama kaƙ zuw kawai kakai kanka Aljann❗yace= wa zai iya yin hakan ya *IBRAHIM* ⁉️ Sai yace= abin mamaki zaka zauna a kasar ALLAH kaci arziƙinsa kazauna a ƙasarsa yan ganinka a ko'ina bazaka iya mayarda Mala'ikan mutuwa ko azaba ba, kuma kazo kana saɓa masa⁉️
 *nan take mutumin yafasheda kuka yace= NA TUBA ZUWAGA ALLAH KUMA NA MIƘA WUYA ZUWA GARESHI*

6️⃣ *-ALHINI*
  Tabbas masarautar BIU da jihar BORNO da ma 9jry munyi babban rashin jajirtaccen jarumi kwamandan *civilian jtf MALIYA* akan hanyar Biu zuwa Danbua, 
  Tarihin Biu bazai taɓa mantawa dashiba don tabbatarda zaman lafiya da kamo boko haram lungu da saƙo a Gombe, Kano, Abuja har Lagos tareda tsabtace cikin garin Biu daga muggan kwayoyi da ƙananan ɓarayi da ɓata gari, 
👏🏻Muna adu'a ALLAH yajiƙansa yagafarta masa yakarɓi shahadarsa yashigar dashi ALJANNAR FIRDAUSI kuma ya albarkaci zurriyyarsa👏🏻
👏🏻Ya ALLAH kaƙarfafi dukkan jajirtattun *civilian jtf* da *sojoji 9jry* da dukkan jami'an tsaronmu kabasu nasara akan dukkan 'yan ta'adda👏🏻
AMIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIN👏🏻👏🏻👏🏻

 _*via👉🏼Abubakar BN Mustafa Biu (ABU-ABDIRRAHMAN)✍️*_
Post a Comment (0)