KHUDUBAR MASJIDIS SALAFIYYA BIU BORNO STATE:
π *02/RAJAB/1443-HJRY
π *04/FEBRUARY/2022-MLDY*
π️ _*GABATARWAππΌAbubakar BN Mustafa Biu*_
⭕ *TOPICππΌ(GOGE ZUNUBBANKA DA TUBA)*
➖ *mun kasashi gidaππΌ 6️⃣*
1️⃣ *-MUQADDIMMA*
Yaku bayin *ALLAH* HaΖika *ALLAH SW* ya halicci bayinsa kuma yasanyasu masu yawan afkawa zunubbaine sai wanda *ALLAH SW* yakuΙutar, shiyasa saboda rahamarsa yabuΙe musu Ζofar tuba da komawa gareshi,
π‘ *ALLAH SW* _<<kutuba zuwaga ALLAH dukkanku yaku muminai donku rabauta>>_ {SRT NUR-31}
π‘ *ALLAH SW yace* _<<kace yaku bayina dasukayi Ιarna kada kuyanke tsammani daga rahamar ALLAH, lalle ALLAH na gafarta zunubbai dukka>>_ {SRT ZMR-53}
Ya Matashi mai saΙon *ALLAH* meyasa bazakayi nadamar laifinkaba kuma katubaba, bakasan *ALLAH* yana farin ciki da mai saΙonda yatuba bane⁉️
2️⃣ *-YALWAR AFUWA DA GAFARAR ALLAH SW GA WANDA YATUBA*
◼️ *SHEIKH KHALID RASHID* cikin littafinsa (Ψ£ΩΩΩ Ψ§ΩΩ
Ψ°ΩΨ¨ΩΩ) yace= *ALLAH SW* yayiwa *ANNABI DAWUD* wahayi cewa- YA *DAWUD* da waΙanda suka juya mini baya zasu san yadda nake saurara musu da tausayinsu da shauΖin barin saΙonsu- da sun mutu don tsananin shauΖina kuma da gaΙoΙinsu ya kakkarye don Ζaunata, wannanfa ga wanda yajuya mini baya to meye tsammaninku ga wanda yafuskanceni⁉️
3️⃣ *-ΖISSAR WANI MAI TUBA*
◼️ *MANSUR IBN AMMAR* yace= nafita wani dare naΙauka asuba yayi ashe baiyiba, sai nazauna jikin Ζaramin wani Ζofa, sai naji sautin wani matashi daga ciki yana kuka yana cewa- da izzarka da Ιaukakanka ya *ALLAH-* saΙawanda nayima banyi son saΙani dakaibaπ’ kuma badon na jahici uΖubarkabaπ’ kuma badon na rainakabaπ’ saidai zuciyatace ta sawwala mini❗kuma shaΖiyyancina ya galabceni❗kuma rufa min asirinda kayi mini yaruΙeni❗ *Ya ALLAH, shin wayene zai Ζwaceni daga azabarka? kuma da igiyar waye zanyi riΖo idan ka katse igiyarka? wayyo ALLAH ina baΖin cikin kwanakinda nashuΙesu a saΙawa ubangijinaπ’ kaicona! na tuba kuma lokaci yayi inji kunyar ubangijinaπ’*
*MANSUR* yace= lokacinda naji kalamannasa daga waje sai naceππΌ
Ψ£ΨΉΩΨ° Ψ¨Ψ§ΩΩΩ Ω
Ω Ψ§ΩΨ΄ΩΨ·Ψ§Ω Ψ§ΩΨ±Ψ¬ΩΩ
π³Ψ¨Ψ³Ω
Ψ§ΩΩΩ Ψ§ΩΨ±ΨΩ
Ω Ψ§ΩΨ±ΨΩΩ
π³ΩΨ§ Ψ£ΩΩΨ§ Ψ§ΩΨ°ΩΩ Ψ’Ω
ΩΩΨ§ ΩΩΨ§ Ψ£ΩΩΨ³ΩΩ
ΩΨ£ΩΩΩΩΩ
ΩΨ§Ψ±Ψ§ ΩΩΩΨ―ΩΨ§ Ψ§ΩΩΨ§Ψ³ ΩΨ§ΩΨΨ¬Ψ§Ψ±Ψ© ΨΉΩΩΩΨ§ Ω
ΩΨ§Ψ¦ΩΨ© ΨΊΩΨ§ΨΈ Ψ΄Ψ―Ψ§Ψ― ΩΨ§ ΩΨΉΨ΅ΩΩ Ψ§ΩΩΩ Ω
Ψ§ Ψ£Ω
Ψ±ΩΩ
ΩΩΩΨΉΩΩΩ Ω
Ψ§ ΩΨ€Ω
Ψ±ΩΩπ³
nan take sai naji sautin Ζara da shure shure mai tsanani, kawai sai natashi nafice, yayinda gari yawaye sai nadawo kofar sai na tarar ana sallar jana'iza a Ζofar kuma ga wata tsohuwa na kaikawo, Na tambayeta- meyafaru? Tace= kada kasabunta mini baΖin cikina, Sai nace= ni baΖone, Sai tace= wannan Ιa nane yarasu jiya da dare yayinda wani (kada ALLAH yasaka masa da alhairi) yakaranto ayarda aka anbaci wuta cikin dare daga bayan Ζofa sai Ιannawa yayita shure shure har yamutuπ₯
*MANSUR* yace= sai nace- _*INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN*_ wannan shine siffar masu tsoron *ALLAH!* Tsarki ya tabbata ga ALLAH wanda yadatarda wasu mutane zuwaga nadama da tuba!
4️⃣ *-TUBA MAGANIN MASU DAMUWA*
Lalle maganin matasa da dattawa masu Ζunci da damuwoyi ayau shine gudowa zuwaga *ALLAH* da kuma haΙuwa da tawagar mutanenda suka tuba suka fita daga duhun zunubbai zuwa hasken tuba kuma suka fifita Aljanna akan Wuta kuma sukayi nadaman saΙonsu,
π‘ *ALLAH SW yace* <<kugudo zuwaga ALLAH>>
π‘ *ANNABI SAW* yace _"nadama tubane"_
π³ *ΖALQU IBN HABEEB* yace= lalle haΖΖoΖin *ALLAH SW* bawa bazai iya sauΖesu dukkaba saidai yayi iya gorgodo kuma yahaΙa da tuba, ba aibi bane yin laifi- aibin shine rashin tuba da kuma dogewa da yin laifin!
5️⃣ *-TAMBAYOYIN WANI MAI LAIFI DA AMSAR WANI MAI HIKIMA*
Wani Mutum yazo wurin *IBRAHIM IBN AD'HAM* sai yace= ya *IBRAHIM-* HaΖiΖa na sabawa kaina da aikata zunubbai da ayyukan ashsha, kagaya mini maganganu masu zafi da zasu ratsani! Sai *IBN AD'HAM* yace= ina maka maka wa'azozi da abubuwa *5*, sai Mutumin yace= kawo na *farkoππΌ*
*[1]- yace=* kadaina cin arziΖin *ALLAH* yayinda zaka saΙa mishi❗yace= ya hakan zai yiwu ya *IBN AD'HAM* tunda shi yake ciyarwa ba'a ciyar dashi⁉️ sai yace= abin mamaki ya zakaci arziΖinsa kuma kariΖa saΙa masa⁉️ Mutumin yace= kawo *nabiyuππΌ*
*[2] yace=* kada kazauna a Ζasar *ALLAH* yayinda zaka saΙa mishi❗yace= ya hakan zai yiwu ya *IBN AD'HAM* tun Ζasar nasane hakama saman nasane⁉️ sai yace= abin mamaki ya zakaci arziΖin ALLAH kazauna a Ζasarsa kuma kasaΙa masa a Ζasar tasa⁉️Mutumin yace= kawo *na ukuππΌ*
*[3] yace=* katafi inda *ALLAH* bazai gankaba yayinda zaka saΙa mishi ❗yace= ya hakan zai yiwu alhali gyangyaΙi ko barci baya Ιaukanshi⁉️ Sai *IBN AD'HAM* yace= abin mamaki kaci arziΖinsa kazauna a Ζasarsa kuma yana gininka duk inda kake kuma kazo kana saΙa masa a idonsa⁉️ Mutumin yace= kawo *na huΙuππΌ*
*[4] yace=* idan Mala'ika yazo karΙan ranka kace dashi= bazan mutu yanzuba❗yace= wa zai iya hakan ya *IBRAHIM⁉️* alhali *ALLAH SW* yana cewa _<<idan ajalinsu yazo baza'a jinkirta musu sa'a guda ba kuma baza'a gaggauto musu shiba>>_ [YNS-29]⁉️Sai yace dashi= abin mamaki kaci arziΖin ALLAH kazauna a Ζasarsa kums yana ganin a ko'ina kuma bazaka iya tunkuΙe mutuwaba amma kuma kazo kana saΙa mishi⁉️ Mutumin yace= kawo *na biyarππΌ*
*[5] yace=* idan Mala'ikan azaba yazo yakaika wuta a ranar Ζiyama kaΖ zuw kawai kakai kanka Aljann❗yace= wa zai iya yin hakan ya *IBRAHIM* ⁉️ Sai yace= abin mamaki zaka zauna a kasar ALLAH kaci arziΖinsa kazauna a Ζasarsa yan ganinka a ko'ina bazaka iya mayarda Mala'ikan mutuwa ko azaba ba, kuma kazo kana saΙa masa⁉️
*nan take mutumin yafasheda kuka yace= NA TUBA ZUWAGA ALLAH KUMA NA MIΖA WUYA ZUWA GARESHI*
6️⃣ *-ALHINI*
Tabbas masarautar BIU da jihar BORNO da ma 9jry munyi babban rashin jajirtaccen jarumi kwamandan *civilian jtf MALIYA* akan hanyar Biu zuwa Danbua,
Tarihin Biu bazai taΙa mantawa dashiba don tabbatarda zaman lafiya da kamo boko haram lungu da saΖo a Gombe, Kano, Abuja har Lagos tareda tsabtace cikin garin Biu daga muggan kwayoyi da Ζananan Ιarayi da Ιata gari,
ππ»Muna adu'a ALLAH yajiΖansa yagafarta masa yakarΙi shahadarsa yashigar dashi ALJANNAR FIRDAUSI kuma ya albarkaci zurriyyarsaππ»
ππ»Ya ALLAH kaΖarfafi dukkan jajirtattun *civilian jtf* da *sojoji 9jry* da dukkan jami'an tsaronmu kabasu nasara akan dukkan 'yan ta'addaππ»
AMIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIIINππ»ππ»ππ»
_*viaππΌAbubakar BN Mustafa Biu (ABU-ABDIRRAHMAN)✍️*_
