Eznah 15

*_EZNAH_*🌹
           _wattpad@mamuhgee_



*15*
Jiki na rawa su Usman suka kwantarda baffa Kan tabarma suka hau you Masa firfita ahankali yafara rage jijjjigar numfashinta ya 'dan farawa rage zaburewar dayayi ya lumshe idanuwansa yayi shiru Yana karanto sunayen Allah a zuciyarsa Dan yasamu nutsuwarsa ta daidaita ya fuskanci Anano Dan haryanxu shi bai yarda da wannan shegen 'dan Mai kukan kwa'di ita ta haifesaba.

Usman ne ya miqe yashiga daki ya qwace Anano daga dukan da aliyu ke Mata cikin tsananin bacin Rai yace,

Wai Kai aliyu meyasa baka auna komai kayisa cikin mizanin hankalin cikakken 'dan Adam ne?

Kana tunanin dukan dakake Mata zaisa ta fa'di gskia ne ko kuwa?
Mitssw''''yaja 'dan qaramin tsaki tareda riqo hannun Anano ya miqar da ita Amma Sam ko tashi Bata iyayi ya miqa hannu zai kar6i yaron tayi saurin 'dago kumburariyar fuskarta ta kallesa saitaga fuskarsa a ha'de ba alamun wasa saita miqa masashi jikinta na rawa gabanta na fa'duwa.

Kwantarda yaron yayi yariqota ta fito tana tafiya daqyar ya kalli jafar da duk yayi zuru zuru yace ya debo Mata ruwa a bokiti tayi wanka.

Ta gefen Inna ta wuce tana kallon yanda innar ke keta faman goge hawaye ta maida kallonta gurin baffa yanayin data gashi acikine yasa hankalinta tashi ta juya 'daki  duk suka bita da kallo

Jaririn ta 'dauko jiki a tsananin sanyaye ta nufi gurinda baffa yake Yusuf yayi saurin daka Mata tsawa Rai a6ace.

Qin tsayawa tayi saidata Kai gaban baffa ta durqusa hawaye nabin fuskarta murya na rawa tace,

Baffa don Allah karka Bari zargi yasa ka cutatar da kanka,
Wallahi wallahi wallahi baffa ban ta6a aikata Zina ba,
Ban ta6a ra6ar ko wani Mai akatawaba,
Wannan jaririn nawa kamar yanda Wadda ta haifesa tabanishi kuma nafada muku da farko Amma wlh baffa bani na haifesa ba.....

Wani mugun kallo aliyu da Yusuf harma da Inna ke binta dashi sbd Jin abinda take fa'da Wai an Bata kyautar jariri.

Baffa kuwa jajayen idanuwansa ya bu'de ahankali ya kafeta dasu cikin rawar murya kamar zaiyi kuka yace,

Anano Abu 'daya nakeson nasani akan jaririn Nan Wanda shika'dai ne damuwata Kuma daga kin fadamin gskia wlh zuciyata Zata iya 'daukar koma meye sauran bayanin
Anano jaririn Nan na waye?

Sabbin hawaye ne suka gangaro Mata ta share murya a dake tace,

taimakon uwarsa nayi lokacinda take naqudarsa Kuma tana haihuwarsa ta rasu.

Tsit sukayi jafar kuwa hambadala yasaki a bayyane aliyu da Yusuf suka bisa da mugun kallo cikin takaici dansu Basu yardaba.

Baffa kuwa tsareta yayi da Ido tsawon lokaci kafin yace,

Anano gskia Kika fa'damin?

Kai ta 'dago ahankali tace eh hawaye na sake gangaro Mata.

Yusuf da Usman ya kalla yace,

Suje inda tafada subi hanyar adubo gawar azoda ita.

Kanta ya maido kallonsa Nan take yaji zuciyarsa ta yarda da ita 'dari bisa 'dari ya riqo hannunta cikin nutsuwa yace,

Anano na yarda dake tako wanne 6angare Kuma natabbatarda bazaki aikata Koda makamancin hakanba Dan haka kiyi qoqarin ganin konan gaba baki rusa yardataba.

Kai ta 'daga ahankali gabanta na fa'duwar wane hukunci baffan zai yanke akan yaron.

Inna ya kalla Koda Bata fa'daba fuskarta ta nuna tashin hankalinta ya 'dan ragu saidai itama kamarsu Yusuf hankalinta bai kwantaba sosai da zancen ananon.

Cikin nutsuwa yace,

Ki tashi ki 'dora ruwa Anano tayi wanka.

Badan tasoba ta miqe ta nufi madafarsu tafara ha'da itace.

Anano kuwa har ruwan yayi zafi tana durqushe agurin Saida jafar ya cika Mata bokiti ya sirka yakai Mata qofar bayi takuna ta miqe jiki a sanyaye ta shiga 'daki ta tube ta fito sum sum tashige bayin.

Duk da tana cikin tashin hankali da damuwar makomar jaririn sosai taji da'din wankan Dan Nan take taji ta'dan warware ajikinta.

Tana gama wankan kafin takai ga fitowa yaron yatashi Nan take ya kara'de gidan da kuka cikin sauri ta janyo zaninta ta 'daura ta fito 
Turus tayi jikinta na saki sbd ganin ba Wanda ya motsa cikinsu kamar basusan da acikin gidan ake kukanba.

Sanyi qalau jikinta yayi Dan kuwa taga tabbas ko barinsa ya zauna gidan baffa yayi bamai qaunarsa.

'dakin tashige bayan ta aje bokitin hannunta ta zauna kusada yaron Nan itama tafara nata hawayen Dan kuwa tasan daga ita harshi suna tsaka.

Saidataji kukan harya fara sanyashi laushi takai hannu ahankali ta 'dauke tareda qura Masa Ido Dan Sai alokacin tafara kallon fuskarsa.

Farine sosai Kuma da gani ba lallaine yayi baqi ba duk da dai bazata iya cewa ga fuskar mahaifiyarsa ba sbd komai yafarune cikin duhu.. 

Numfashi ta sauke ahankali cikin zuciyarta tace,

Allah yasa su hamma su gano gawarta asuturta kodan jaririn.

Sallama aka fara kwadowa a qofar gidan baffa ya kalli qofar da sauri zuciyarsa na 'dan tsinkewa ya miqe daqyar tareda tattaro 'yar nutsuwa ya nufi qofar aliyu nabin bayansa.

Murmushin qarfin hali yasaki lokacin dayaga Mal Garba maqwafcinsa yace,

Aa Mal Garba Kaine da safennan.

Cikin 'yar damuwa yace,

Nine Mal salisu an gari lafiya?

Lafiya qlau Mal Garba ya iyalin?

Alhamdulillah nace ko anji want bayani akan Anano kuwa?

Washe baki baffa yayi cikin qarfin hali yace,

Eh kaga shaf na manta na sanar maka tun a Daren jiyan tadawo Wai Ashe ita da qafa ta qaraso daga can rugar nuhu shiyasa ta iso dare sosai.

Masha Allah Abu yayi kyau dama dai nace ne nazo naji halinda ake ciki Kan 6atan nata Allah ya tsare gaba.

Amin Amin Mal Garba nagode.

Bayan tafiyarsa baffa ya Jima tsaye Yana tunani kafin suka juya suka koma cikin gidan Kai tsaye inna ya kalla yace,

Ki kimtsa yaron ki goyesa duk tsanani Kar kibari agane da akwaisa acikin gidannan.

To tace badan ranta yasoba saidan Bata qetare umarninsa ta miqe ta sake 'dora wasu ruwan.

Cikin qanqanin lokaci Inna tayi Masa wanka ta gasashi sosai ta 'debi sabuwar madarar shanu tabasa yasa sosai Nan take yayi luf bacci Mai da'di ya daukesa takuwa goyesa bayanta tasaka hijab bazaka taba cewa akwai 'da a bayanta ba.

Sai alokacin Anano ta'danji sanyi aranta take Kuma mamakin yanda takejin yaron har tsakiyar ranta.

Kamar jira ake Inna ta goyesa Nan take jama'a suka fara zaryar zuwa barka da dawowarta dakuma ganinta da'akayi.

Su ubaidah sunxo Nan suka hauta da fadan tafiyarta datayi Bata tsaya musu ba.

Itadai murmushin yaqe kawai take musu
Koda suka tambayi kumburin fuskarta da Jan idonta cemusu tayi batai bacciba ahanya qunama ta cijeta.

Sosai suka tausaya Mata duk da sun fahimci kaman Bata cikin walwala hakanan suka qarashi firarsu suka tafi.

Su Yusuf kuwa duk iya bincikensu Basu ga wata gawaba haka suka dawo suka sanarwasu baffa qarshe dai aka tattara zancen aka aje Sai bayan kwana biyu tukuna a yanke shawarar abinyi.

Tunda tadawo kusan komai ya canxa Mata ba kamar da ba da kowa gidan keji da ita kamar su lasheta Amma yanxu kaf yayunta iyakacinsu da ita ta gaidasu idansunga dama su amsa idan basuga damaba su qyaleta baffa da jafar ne kawai ke kulawa da ita Sai Usman idan yaga dama shima,

Inna kuwa kadaran kadahan ga baffa dayasata kulada jaririn Dole badan tasoba.

Sosai hankalin ananon hankalinta yafara 'dan kwantawa sbd ganin anbar zancen saigashi Randa sukai sati 'daya kwatsam zancen yafara fita Wai akwai jariri agidan Nan maganganu suka fara yawo hankalin baffa yafara tashi musamman da zancen yafara yaduwa Wai 'dan na Anano ne tunda dai ba Wanda zai haihu a gidan.

Zaune suke a tsakar gida yau duk sunyi jugum jugum bamai magana Sai Inna daketa aikin Kai kawon girkin dare datakeyi Anano kuwa tana zaune tana yiwa Inna wanke wanke jiki a sanyaye sbd tun Daren jiya taji hirar Inna dake bawa baffa shawarar akai yaron gidan Mai gari ace tsintarsa akayi.

Cikin sanyin murya baffa yace,

Idan muka kaisa mukace tsintarsa mukayi kenan mun bada damar daza'a yarda da zargin da ake Mana sbd zaaga meya Hana tun farko mukaisa Saida aka ganomu,

Kawai dai na yanke shawarar aikasa can binni gidan marayu kamar yanda Yusuf yace tun farko.

Da wannan tunanin ta kwana ta tashi sosai taji hankalinta yatashi sbd tausayinsa dakuma qaunarsa dake maqale aranta.




# vote
# comment
# share


Post a Comment (0)