TAMBAYA TA 381

*Tambaya ta (381)*
:
_Mace ce Mijinta yasadu da'ita amma kafin tayi wanka sai Haila tazo mata, Shin wanka biyu zatayi kenan ko yaya?_
:
*_Amsa_*
:
_*Alal-Haƙiƙa* ansamu *Saɓānin Mālamai* dangane da hukuncin Matar da tasadu da Mijinta kokuma tayi mafarki amma kafin tayi *Wankan-Janaba* sai *Jinin-Haila* yazo mata, kokuma yakasance Mace tana cikin *Jinin-Hailarne* kuma sai tayi mafirki har Maniyyi yafito mata,_
:
_*Mazhabin Hanābila* dakuma wasu daga cikin *Mālamai* suntafi akan cewa ba wajibi bane akanta tayi sai tayi *Wankan-Janaba,* danhaka zata jirane harsai *Jinin-Hailar* yaɗauke sannan tayi wanka, amma inda zatayi *Wankan-Janabar* alokacin datake *Jinin-Hailar,* shikenan wankanta yayi kuma hukuncin janaba yasauka daga kanta, shikuma *Jinin-Hailar* hukuncinsa yana tare da'ita harsai idan ya yanke sai tayi masa wanka, amma idan batayi *Wankan-Janabarba* harsaida *Jinin-Hailar* yaɗauke mata, mafi yawan *Mālamai* waɗanda suka haɗa harda *Mazhabobin nan guda huɗu sanannu,* suntafine akan cewa idan tazo wankan zata ƙulla niyyar *Wankan-Janaba* da *Wankan-Haila* azuciyarta saitayi wanka guda ɗaya ya wadatar, amma wasu daga cikin *Mālamai* suntafine akan cewa dolene sai tayi wanka biyu kowanne nasa dabam, saidai maganar farko da'akace zatayi wanka ɗayane da niyya biyu tafi inganci,_
:
_Amma *Mazhabin Mālikiyya dakuma Hanābila* sukace idan da zata ƙulla niyyar *Wankan-Janaba* kaɗai azuciyarta ko *Wankan-Haila* kaɗai, to iya abinda ta *ƙulla niyyar* akansane kawai yagushe daga gareta banda ɗayan, domin *Mαиzoи Aʟʟαн(ﷺ)* Yace:_
:
*"إنما الأعمال بالنيات، وإنما لكل امرئ ما نوى"*
*_MA'ANA:_*
*_Lallai ayyuka (na ibada) saida niyya, kuma kowanne mutum (ana karɓar aikin) da yayiwa niyya ne,_*
:
_Saidai *Mazhabin Shāfi'iyya da Hanafiyya* sukace koda niyyar wanka guda ɗaya kaɗai ta ƙulla azuciyarta sukace yayi saboda zai iya ɗauke hukuncin ɗaya wankan, to amma maganar *Mālikiyya da Hanābila* tafi inganci dakuma Dalili mai ƙarfi,_
:
_Danhaka magana mafi inganci wacce mafi yawan *Mālamai* suka tafi akanta shine, idan *Jinin-Haila* yazowa mai Janaba kokuma Janaba tazowa mai Haila, to zata dakatane harzuwa lokacin da *Jinin-Hailar* zai ɗauke mata, sai ta ƙulla niyyar *Wankan-Janaba* da *Wankan-Haila* azuciyarta sai tayi wanka guda ɗaya ya isar mata,_
:
*_※(шαʟʟαнυ-тα'αʟα α'αʟαмυ)※_*
:
*_ωαηαη sнιηε gωαяgωαdoη ɗαη αвιηdα ιʟιмιη мυ dαкυмα вιηcιкεηмυ үαкαι zυωα gαяεsнι, dαηнαкα ιdαη αηgα ωαηι кυsкυяε αcιкιη αвιηdα мυкα яυвυтα тo αηα'ιүα ғαɗαкαя dαмυ мυgүαяα, тαяεdα кαωo нυננα мαι ƙαяғι:_*
:
*_Doмυп пεмαп ƙαяıп вαчαпı sαı αdυвα шαппαп ʟıттαғı καмαя нακα:_*
                 *_↓↓↓_*
:
*"المغني لإبن قدامة" (1/135)*
*_▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂_*
              *Daga Zaυren*
             *Fιƙ-нυl-Iвadaт*
*_▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂_*
              *_→AMSAWA←_*
           *Mυѕтαρнα Uѕмαи*
              *08032531505*
*_▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂_*
_*Doмιɴ ѕнιɢα ѕнαғιɴмυ dαкє ғαcєвooк ѕαι αѕнιɢα wαɴɴαɴ lιɴк кαwαι αyι ""lιкє""👇🏾*_
:
https://m.facebook.com/fiqhul.ibadat/

Post a Comment (0)