TUN KAFIN AURE 34

TUN KAFIN AURE💐34



Yadda tayi zurfi a tunani yasa Junaid kare mata kallo. Wayarta ce ta hau tsitsi shi ya dawo da ita daga dogon tunaninta. Da sauri ta dauka ganin baffanta ne. Tana masa sallama yace Hafsa ya jikin? Dazu babanku yayi min waya kinji ciwo. Ince ko babu wani mugun rauni..dariya tayi ashe kana sona dai Baffa. Yayi dan gyaran murya kaniyarki wasa nake dake ne. Ta sake wata dariyar baffa babu ciwo sosai glass ne ya shige min kafa amma an cire. To sannu Allah Ya kara sauki, amma ki rinka kula kinji ko. Ga Mamanki duk ta damu itama. Sun dade suna hira da mama da kannenta kowa yana mata sannu. Bayan ta gama wayar yace yanzu tun dazu ina magana kina share ni sai da kika ji muryar su baffa kika yi dariya ko. Yadan bata fuska kamar zaiyi kuka Allah Sarki Junaid babu mai sonka. Har tissue yasa yana goge ido , bata san lokacin da dariya ta kubuce mata ba. Wayarta ya dauka yana juyawa. Ni na gaji da ganin wannan toy din. Idan munje gida kizo ki karbi sabuwar dana siya miki. I hope you will like it.

Bayan yayi parking din motar Hafsi ta bude zata fito yace tsaya ina zuwa. Zagayowa yayi ga mamakinta sai kawai taji ya dauketa. Yau karo na uku kenan yana daukarta. Tana ta mutsu mutsu ya ajiyeta kada wani ya gansu ya share. Da kafa ya tura kofar motar bai tsaya ko ina ba sai a side dinsu dake bayan gidan. Ajiyeta yayi ya bude kofar ya sake daukanta, kan doguwar kujerar falo yasauke ta ya duka hannunwansa duka biyu a gwiwoyinsa yana ta nishi. Wai Hafsi haka kike da nauyi...anya baki kai buhun shinkafa biyu ba kuwa. Filon kan kujerar ta jefa masa wallahi bani da nauyi. Kuma ma ai bance ka daukeni ba. Ya sami wuri kusa da ita ya zauna tare da janyota jikinsa. Gaskiya yarinyar nan idan kika hau kaina buzu na zaa dauka. Mintsini yaji a gefen cikinsa tace ya fa isheka ko don kaji ina shiru. Ya kama gefen cikin ke dama haka kike? Don kin kone a ciki nima nakasa ni zakiyi. Ya danyi murmushi me kama da na mugunta kinsan fatar cikinki zata fi dadin mintsini ko. Tana jin haka tayi saurin tashi sai ta fada jikinsa saboda zafin da kafarta tayi. Rungumeta yayi sosai hmmm su Hafsi wayon ki dan ji dumin jikina shine kika wani fado min a jiki. Maganar da tayi niyar yi ce ta makale mata saboda kunya data kama ta. Zata bashi hakuri taji ya hade bakinsu wuri daya. Cikin kankanin lokaci suka tafi wata duniyar sai dai basu dade ba suka ji bugu a bakin kofa tare da sallamar Hamida cikin daga murya.

Tsaki yayi ya amsa mata tare da mikewa. Tace Yaya munji shigowar motarka amma har yanzu Hafsi bata shigo gida ba. Wani tsakin yayi gata nan zuwa kill joy sim dinta zan saka a sabuwar waya. Hafsi dai gintse dariya tayi don yadda taga yana bin Hamida da harara bayan ta rikota zata taimaka mata su koma cikin gida.




Batul Mamman💖

Post a Comment (0)