Eznah 25


*_EZNAH_*🌹
        _wattpad@mamuhgee_




*25*
Zuciyarta taji tana sake kar6ar komai ta bu'de idanuwanta ahankali tareda kallon zayyan tayi shiru batareda tayi maganaba....

Shima ita yake kallon yace,
Trust me Anano I will never let anyone hurt you,,,,
I will never let any harm cme to you insha Allah....

Saheeb is my only family my only friend...
Muna secondary School na rasa both mum Dina da dad,
Saheeb shine yaci gaba da daukar nauyin karatunmu harmuka gama muka shiga military school.....
Saheeb has always been there for me harnakawo matsayin danake dashi yanxu nazamo wani.

Saheeb tun Yana yaro yataso cikin wata irin rayuwar kadaici da Rashin farin ciki sbd tsawon rayuwata da saheeb banta6a ganinsa cikin farin cikiba,,,,,
He was living a loneliness life,,,
A with no one to care or been there for him,
Tun muna yara Sam shi ko wasa bayayi sbd that witch woman tariga ta kashe Masa rayuwa and Abba is always busy he has no time for him,
Baisan damuwarsa ba,baisan buwatarsa ba,baisan ciwonsaba baisan farin cikinsa ba..

Nafeesat in his life was the only first good thing that happens to him sbd yafara hangowa kansa sauyin rayuwa,rayuwar farin ciki da iyalansa sbd samun cikinta changes alot Amma saigashi lokaci 'daya sun rabasa da wannan farin cikin, again he lost all hope haryana tunanin baya cikin masu rayuwar farin ciki a duniyar nan....

Anano Insha Allah kece hasken rayuwar saheeb daya Dade baizoba,

Kallonsa tayi idanuwanta na bushewa Jin irin rayuwar da saheeb ya 'debo shekaru yanayi haryanxu..

Share hawayenta tayi cikin wata irin murya tace,

Kamar yanda tafada Zan tabbatarmada gaskiyar hakan datace lallai 'dan iska na qauye..

Kallonta yayi ganin yanda tayi maganar koba komai tafara soye zuciyarta Wanda Dole saita cire duk wani tsoro ta qeqashe zuciyarta kozata iya hakan
Hakama Dole zata cigaba da karatu sbd samun cikakken ilimin dazata iya kane kane da dukiyar tahana kowa iko da ita sbd har Abba Dole zai shiga layi coz idan ba haka mum asee zata riqa amfani dashine tana samun yanda takeso...


Kodata suka rabuda zayyan tadawo 'daki ta 'dauki abdulshakur dake wasa  ta rungume jikinta tareda lumshe idanu tanajin sabuwar qaunar yaron nashigarta sbd taqara tabbatarda shine qaddararta tunda samunshi shine mafarin komai...

Kallo 'daya gwaggo tayi Mata ta 'dauke Kai sbd ita alamarin Ananon yadaina Bata mamaki.

Da daddare harta kwanta Amma takasa bacci
Zuciyarta takasa samun sukuni Sai azalzalarta takeyi akan tunda tana zargin zamowar Abdul 'dan nafeesat to tabbas idan batai bincike ta tabbatarba to Sam baymtayiwa Abdul adalciba..,
Meyasa tasawa Abdul suna abdulshakur sbd mahaifiyarsa ta fa'da Mata sunan mahaifinsa ne....

Tashi tayi zaune gabanta na tsananta fa'duwa tareda saukowa ta nufi akwatin kayanta ta bu'de ta fiddo komai kafin taciro wani qyalle ta warware zobenda uwarsa tabata ya bayyana..

Qurawa zoben idanuwa tayi tanajin fargaba nacigaba da shigarta ta rintse idanuwa tareda miqewa ta fito dakin ahankali...

Qurawa qofar kicin dinsa idanuwa tayi na tsawon mintuna tana qara qame zoben dunqule ahannunta..

Cikin fargaba da wasi wasi ta nufi qofar ahankali takama handle din ta bu'de tareda shigewa....

Kamal da dawowarsa kenan daga yawonsa a buge yake Amma duk da haka saidaya zagayo da niyyar nemanta cikin Daren danya lallasheta Sai kawai yaga shigewarta qofar kicin din part din saheeb na bayan....

Ransane yayi mummunan 6aci zuciya ta ciyosa ya juyo Yakoma part dinsu mum asee yaci sa'a palon ba'a saka key taciki ba...

Kicin ya nufa direct yafara 6arin Kaya gurin neman wuqa Dan ya'dau alwashin kashe saheeb yau kowama ya huta....

Yakurah cikin bacci taji 6arin Kaya ta zabura zaune gabanta na fa'duwa ta sauko gadonta ahankali tareda fitowa bedroom 'dinta ta nufi kicin din cikin san'da...

Cak ta tsaya cikeda mamaki da tashin hankali kafin taqaraso da sauri ta riqesa tana Kiran sunansa...

Zuciya a qone yace,

Wai Ina kuka aje wuqaqaen gidan Nan ne you fools..

Riqesa tayi da qarfi tareda jijjigasa tace,

Wai meyene?kafadamin saina nuna ma indasuke..

Wani mugun kallo ya watsa Mata da jajayen qananun idanuwansa cikin zafi yace,

That bastard has been seeing my girl tsawon lokaci mum tasa nay shiru and now har cikin dare Yana tareda ita Yana samun ni abinda bansamuba wlh kashesa zanyi kowama ya huta idan bamu samu dukiyarsa Yana raiba ai idan ya mutu munci gado...

Wani wawan kallo yakurah tasakar Masa tana cewa,

To idanma Dan wannan ne tun wuri saika shirya Dan kuwa bashi ka'dai zaka kasheba har mum asee sbd kuwa taha'da plan din komai na ha'dashi aure da anano Kuma cikin gaggawa batareda tayi la'akari da anano takaceba.....

Shaqota yayi da qarfi cikin zafin Rai yace,

Don't you dare say that nonsense ag.....

Daqyar ta bu'de baki tace,

Let go off m you bastard am not talking any nonsense.....

Sakinta yayi cikin hasala ganin tana neman rasa numfashinta Dan muguwar shaqa yayi Mata.

Tari tafara tana shafar wuyanta kafin takallesa da jajayen idanuwanta dasuka fito tace,

You stupid ingreat this anger will kill you one day.,

Cikinta yasake yowa aharzuqe tayi saurin ja baya tana cewa,

Karka sake gigin ta6a lafiyata Kuma wannan fushin ba'anan zaka nunaba save it for your mamah Dan idan bakayi da gaskeba kanaji kana gani zata rabakada Anano,she just don give a damn about you....

A hasale ya ture kayan dake gabansa na glass Yana fidda wani irin hucin 6acin Rana Yana cewa,

Hakan bazai ta6a faruwa ba.....

Ganin ya haukace Sai wurgi yake da kayan kicin din tayi saurin dauko wayarta ta dannawa mum asee Kira.

Mum asee cikin bacci taji ringin na wayarta ta bu'de idanuwanta Sai Kuma tajiyo kamar 6arin Kaya da sauri ta miqe tareda kallon Abba daya saki jiki Yana sharar bacci tasauko gadon ahankali riqeda wayarta ta fito 'dakin ta sauko qasa da sauri...

A palo yakurah tayi saurin tareda tana cewa,

Mum Kamal is completely crazy yanason 6ata Mana plan ne....

Kallon qofar kicin din tayi kafin ta nufa qofar tana cewa,

Bar shegen maganinsa zanyi da tosashiyar kwakwalwarsa..

Kallo daya ta Masa ta 'daure fuska cikin tsananin bakin ciki da mamakin haukardayayi akicin din duk tana tunanin a buge yake.

Gabanta yazo ya tsaya cikin zafin zuciya yace,

Duk Wanda yace zai shiga tsakanina da abinda nakeso sainaga bayansa...Dan kuwa Anano tawace Bata uban kowaba.,

Takaicine yazowa mum asee wuya sbd itadai kowa yafita samun 'da wannan toshewar kansa hartafi qarfin tunaninta..

Danne 6acin ranta tayi sbd wannan fushin nasa dashi zatayi amfani takaiga cimma auren Anano da saheeb.
Cikin kulawa takallesa tace,

Kamal wayace maka rabaka za'ayi da anano,
Ni kaina Ina tsananin sonka da ita musamman kawai Dan farin cikinka....

Sbd farin cikina shine Zaki hadata aure da bastard son dinki batareda sanina......

Karkace haka Dan kuwa a shirye nake dana tsaya nayi fito nafito da kowa akan farin cikinka Dan haka kaima nake fa'da maka karkayi Sanya ka 'daga hankalin kowa musamman abbanku kace Sam baka yardaba saheeb na nemar maka matarda kake aure Kuma ka tsaya tsayin dakan kasha kamasa Yana ja maka ita part dinsa....

Harsainayi qarya tunda dai hakan tana faruwa a idona nagani yanxu hakama tana gurinsa Nagani
I will kill her this.....

Kamosa mum asee tayi takawo har qofar Palo ta bu'de ta fitar dashi tace,

Sbd toshewar qwaqwalwarka shine kazo Nan mu zakayi Mana hauka to kaje can inda ake cin amanar taka kasamu ka'dau shaidar dazata fitarda Kai gobe Dan kuwa gobe duk ubanda ya tsaya kace baka yardaba saheeb nemarma matarda zaka aura yake.

Tana fa'dar haka kuwa takoma palon ta rufe qofar tareda yiwa yakurah kallo 'daya ta wuce sama tana jinjinawa daqiqancin da Allah ya wadatar a kwanyar 'danta.

Shikuwa a fusace yabar gurin ya nufi part din saheeb Yana fatan yatarar dasu a wani mugun yanayi acikin Daren zai watsasu a Media a qarasa kwace sauran two star dinsa kowama ya huta.



Tunda tashiga palon take takawa ahankali gabanta naci gaba da tsinkewa,,

Ahankali ta lalubo switch ta kunna wutar palon tafarabin palon da kallo ta tsaida kallonta gurin qofar datasan qila nannan bedroom din matar saheeb data rasu..

Rintse idanu tayi tareda sauke numfashi ahankali kafin ta bu'de ta nufi qofar ta riqe handle din ta bu'de ahankali tareda gabanta na fa'duwa tashiga ta lalubi switch gurin qofa ta kunna Nan take tasaki qaramar ajiyar zuciya ganin batai kuskure ba Dan kuwa Dana saheeb ne tabude batasan yazatayiba acikin Daren.

Abinda tazo nema shita hango ajiye akan bedside drowr cikin wani Dan frame Mai girma ta tsaya cak tana tsoron dubawa Sai Kuma ta nufi gurin takai hannunta dake rawa ta 'dauko hoton tareda Kai kallonta ga hannuwan nafeesar dake tallafe da kumatunta duka tana murmushi gashi hoton  ya 'dauku matuqa..

A hannuwan nafeesar takai kallonta tareda qara matso da hoton fuskarta jikinta na qoqarin saki...

Hannunta tabude takalli zoben kafin tasake maida kallonta ga yatsun nafeesat ta qure idanuwanta
Nan take tasaki hoton taredayin baya sbd shakka Babu ta tonowa kanta masifa Dan har cikin ranta Bata fatar Abdul yazamo nasu Dan batasan ita kanta yazata qare dasuba bareshi da idan sukasansa ba abinda zai Hanasu rabasa da duniya Sai Allah....

Hawaye taji sun 6alle Mata amaimakon tayi farin ciki saitaji tana danasanin dubawar duk da tana qoqonto tunda ba DNA bane Amma tabbas ba shakka abdulshakur Dan saheeb da nafeesat ne.....

Motsi taji abayanta da sauri ta juyo jikinta na rawa tanajin anturo qofar 'dakin tayi saurin shigewa cikin qatuwar wardrobe din dakin zufa na karyo mata....

Tunda yashigo ya hango hijabinta tacikin wardrobe yafito Nan take ransa yaji Yana quna sbd Sam yakasa gane inane gabas inane kudun wannan yarinyar Amma zaiyi maganinta once and for all ya huta...

Tsayawa yayi tareda qurawa hoton data yarda qasa Ido Nan take idanuwansa suka canza wani irin zafi da nauyi suka ziyarci zuciyarsa ya lumshe idanuwansa Yanajin kewar nafeesat da cikinsa na qara shigarsa....

Bu'de idanuwansa yayi tareda bu'de wardrobe din da qarfi ya fixgota notee nacikin wardrobe yariqe hijab 'dinta Amma sbd fixgar dayayo Mata Bata hankali bace Sai hijab din ya 6arke gaba daya ya maqale aciki ta fa'do Masa ya kauce da qarfi arashi  shiri Sai su dukan sukayi baya suka zube a gadon dake bayansa na dakin....

Kamal daya shigo cikin san'da ya hango qofar dakin a bu'de yaqarso da sauri....
Zuciyarsa tayi wani mugun daukar zafi ya fiddo wayarsa tareda maqalewa gefe yafara daukrsu...

Shine aqasa itace ta fa'da samansa
Doguwar Rigar bacci ce ajikinta ko hannu batada gata batada nauyi ko ka'dan Sai santsi gashi ko hula batada akai..
Shikuwa dogon wandon kayan baccine ajikinsa black da black vest data Kama qaqqarfan jikinsa...

Wani wawan turi yai Mata tafadi gefe itama batai wata wataba ta miqe tareda fisgo hijabin daya maqale tayi qofa da gudu tabar part 'dinsa gaba daya.

Dafe goshinsa yayi tareda futarda wani zazzafan numfashi yanajin wani irin tsanar zaman gidan
Dole yashirya yaje dogon hutu kozai samu nutsuwa..

Tunda takoma takasa kwanciya ta nemi guri ta zauna tareda rafka uban tagumi tana tunanin abinyi akan wannan tsaka Mai wuyar....

Cikin bacci gwaggo tabude Ido taganta zaune da uban tagumi tace,

Da wannan tagumin da tashi kikayi Kai tsayuwar dare ko Allah zai kawo nutsuwa da hankali cikin kanki Dan ni wannan alamarin naki saina hada da magungunan daji...

Tabbas gwara tayi tsayuwar dare ta roqi Allah mafita Dan kuwa tana neman mafitar..

Tunda tafara salloli Bata tsayaba saidataji anfara Kiran asuba tayi tazauna ta roqi Allah akan yasaka Mata dauriya da juriya tareda bushewar Ido akan wannan alamarin Dan kuwa matuqar ba hakan tazamo ba su mum asee zasuci galabarta Kuma Dole ta kiyaye Babu Wanda zausan waye abdul,
Bazata ta6a Bari wani yasanda wannan sirrinva har zayyan Dan kuwa ta'dau alqawarin barwa kanta zobenma tamaida can kasan Kaya ta boye....

Da safe kallo daya tawa Abdul Nan take tafara hango kamanninsa da nafeesat Bai dauko komaiba na saheeb Sai hasken fata da dogon hancin...

Rungumesa tayi ajikinta tanajin tausayinsa na qara shigarsa sbd ga iyayensa tafara ganowa Amma ba damar ahadasa da mahaifinsa sbd tarin maqiyan mahaifin nasa....
Abdul koban Kare saheeb Dan komaiba Zan tsaya na karesa kodan kasancewarsa uba agareka 'dana.

Wanka tayi tayi Masa wanka suna cikin shiri gwaggo tashigo da tea ahannunta tana cewa,

Megida zoga shayin ka..

Lafewa yayi jikin ananon Yana maqalewa gwaggon kafada..

Kajimin tsohon Dan dabara yau ni kakewa wani Jan aji Dan kaga firgitacciyar uwarka na kusa....

Karbar tea din Anano tayi tana cewa,

Gwaggo qila da zafi kike basa shiyasa..

Da wuta nake basa qarewar zafi...

Dariya tayi tareda Dan zaro idanuwa tana cewa,

Haba Gwaggo da gske wuta kike basa,
Gske dai Naga yarona Yana Zama jarumiba kullum...

Muguwar harara gwaggon tasakar Mata tareda miqewa tashige toilet tana cewa,

Shegen gorar zai zamo jarumin ne idan ya nemi nabasa abinci abaki naqi..


Qarfe Tara Kamal ya fito daga part dinsa ya nufi 6angarensu mum asee har lokacin xuciyarsa Bata saukaba danma tun jiyan ko rintsawa yakasayi yanda yaga dare haka yaga safiyar badan Yana tsoron sojojin saheeb dinba datun a Daren jiyan zai 6arkawa kowa rigar mutunci acikin gidan Amma wlh yau Sai anyita ta qare....
Mum asee takirasa da sakarai akan bazai iya daukar mataki akan alaqar saheeb da ananoba toyau zai nunawa kowa bamai Anano saishi.


Zaune suke suna breakfast a dining
Abba abincinsa yakeci hankali kwance
Mum asee cin Dole kawai take tana fatar tarkon data nadawa Kamal jiya na kunnosa Akan Anano da saheeb yayi Dan yazo yatada rigima tasamu shigowa da Tata buqatar.

Banko qofar palon yayi ya nufo gurinsu cikin zafi...

Kallo 'daya mum asee Tama yakurah
Nan take ta miqe ta nufi Kamal din tana cewa,

Kamal lafiya ku.....

Bata qarasaba ya tureta cikin bakin ciki tareda cewa,

Duk gidannan munafukaine da kafurai aciki harma da azzalumai to kowama yasani nagaji da hakuri kodai Abba yadau mataki Kona dauka da kaina.....

Da sauri mum ta taso cikin tashin hankali takamo yakurah dake kukan qaryan turan da Kamal yamata tace,

Me akai maka kaketa wannan tashin hankalin Kamal?

Karma ki tambayeni Dan wlh a shirye nakeda nayi komai agidannan..

Masifa da rashin mutumci yafara zubawa musu a palon tako ina

Abba ya qaraso da sauri shima Jin alamarin yafara tsananta Dan kuwa harda Mari mum asee ta sakar Masa...

Cikin tashin hankali Abba yakalli Kamal daya taba kumatunsa yaqara harzuqa yace,

Duk Wanda zai mutu ya mutu wlh bazan yardaba..
Abba matar danake Shirin aurece kullum saheeb ke kiranta part dinsa sunacin amanata batun yanxu nake kamasuba Amma yaqi Bari to wallahi koka dauki mataki Kona yadasu a duniya kowa yasani mutuncin gidannan ya Dade Bai zubeba matuqar ba"a dau matakiba...

Cikin takaici mum asee tace,

Kamal bance karka fitar da zancen nanba gashi yanxu kana neman zubar Mana da mutunci da 6ata Mana suna
Me kake tunanin za'a riqa kallon saheeb dashi agari ace Yana neman matar qaninsa alhalin ko gama farfadowa baiyiba daga wancan iftila'in na kwanaki......

Katseta Abba yayi cikin fargaba da mamaki da cewa,

Wace matarce wannan ni ake magana..

Anano""""Kamal yafada Kai tsaye Yana cewa,

Wllh wuta zan kunnawa motocinsa kowama ya huta....

Tsawa Abba ya daka Masa Yana kallon mum asee datayi qasa dakai cikin jimami yace,

Aseeya me nakeji Yana fa'da?

Cikin nuna takaicinta tace,

Alhaji wlh nayi iyayina gurin Hana hakan gashi shi wannan Mai zafin zuciyar Sai tashin hankali yake yanason Bata sunan gidan Nan nidai wannan alamari bansan yazamu 6ullo masaba.....wannan masifa Dame tayi Kama..

Asabe Abba ya qwalawa Kira cikin zafi yace taje takira Masa saheeb da anano harma da gwaggo..

Da gudunta taje Kiran saheeb tafadawa yaronsa daya yace zaije yanxu yasanar Masa
Taje tasanardasu Anano cikin tsananin mamaki suka biyota ba 6ata lokaci...


Suna shigowa ko gaisuwar gwaggo nai amsaba yakalli Anano yace,

Meke tsakaninki da saheeb?

'dagowa tayi da sauri Sai mum asee tayi Mata wani kallo takalli abban tareda sunkuyar dakai qasa cikin wani irin yanayi tafara hawayen data qirqiro Nan take tace,

Abba Dan Allah kayi hkr ba laifina bane shine yake kirana.....

Wani sabon mamaki da takaicine ya rufe abban kenan dai da gaskene abinda ke faruwa.....

Waya Kamal yafitar cikin takaici ya nunawa Abba hotunansu na jiya Yana cewa,

Wlh andai cuceni ancuci rayuwar yayanda Zan Haifa....

Wayar Abba ya karba tareda miqawa saheeb din daya shigo cikin fararen qananun Kaya hannu yakai ya karba wayar sbd baisan meke faruwaba

Kallo daya yayiwa hoton ya 'dauke Kai tareda tsuke fuska yakalli gefen Anano Yana watsa Mata mugun kallon tuhuma....

A zafafe Abba yace,

Yimin bayanin abinda hotunan Nan ke nufi..

Kallon abban yayi da sauri Dan Bai tsammanin Jin hakanba.

Kuka Anano tasaki harda shesheka tace,

Abba Dan Allah kayi hkr karka Hana aurena da Kamal wannan qaddarace ta gifta tsakanina da saheeb Kuma Allah nidai nayi nadama....

Cikin zafi mum asee tace,

Ba Wanda zai aureki cikin yayana sbd bazan taba yardaba kizamo matar yayanaba.....

Cikin kuka Anano ta rarrafo gaban Abba hardasu shaqewa tana cewa,

Abba Dan Allah ayimin adalci sbd bani kadaici Mai laifiba Kuma qaddarace Kuma kunada 'ya mace gatanan idan akayimin rashin adalci Allah bazai Bariba yunda mace Bata 6anna ita ka'dai....

Tabbas mace Bata banna ita ka'dai shiyasa Nima bazan bar Mai laifiba yaje abanxa
Aure kuwa tsakaninki dashi ai Dole ayi tunda haryasan ya nemi matar Da Dan uwansa zai aura ai Dole ya aureta....

Zaro idanuwa Kamal yayi tareda zaburowa Abba ya 'daga Masa hannu tareda kallon saheeb yace,

Duk Wanda na Haifa na isadashi bazaiyi magana akan wannan aurenba Kuma na rufe mgnar anan Kar akuma tadata sati biyu masu zuwa za'a daura aure...





Comment
Vote
Share
Post a Comment (0)